Coronavirus: Har yanzu ban warke ba - El-Rufai

Gwamna El-Rufai

Asalin hoton, KADUNA STATE GOVERNMENT

Bayanan hoto, Gwamna El-Rufai ya ce shi da kansa zai fito ya fada wa duniya idan ya warke daga cutar korona
Lokacin karatu: Minti 1

Gwamnan jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya, Nasir Ahmad El-Rufai, ya ce har yanzu bai samu sauki daga cutar korona ba.

El-Rufai ya bayyana haka ne a sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter da yammacin ranar Laraba.

"Har yanzu ban warke daga cutar covid-19 ba kuma da kaina zan bayyana hakan idan na warke. Ku guji yada labaran karya ko da kuwa kuna son yi," in ji gwamnan.

Kauce wa X, 1
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X, 1

A ranar Laraba ne, gwamnatin jihar ta ce ta sallami mutum daya cikin mutane shida da suka kamu da cutar korona a jihar.

Gwamna El-Rufai ya sanar da cewa ya kamu da cutar korona ne ranar 28 ga watan Maris.

Karin bayani kan coronavirus
Karin bayani kan coronavirus

Sai dai gwamnan ya ce har lokacin bai fara nuna alamun cutar ba amma ya killace kansa.

Kauce wa X, 2
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X, 2

Sauran su ne:

Abba Kyari - Shugaban Ma'aikata a fadar gwamnatin Najeriya

Bala Muhammad - Gwamnan Bauchi

Seyi Makinde - Gwamnan Oyo

Muhammad Babandede - Shugaban hukumar kula da shige da fice

Sai dai tuni Bala Muhammad, Seyi Makinde da Muhammad Babandede suka bayyana cewa sun warke daga cutar korona.