Coronavirus: Har yanzu ban warke ba - El-Rufai

Asalin hoton, KADUNA STATE GOVERNMENT
Gwamnan jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya, Nasir Ahmad El-Rufai, ya ce har yanzu bai samu sauki daga cutar korona ba.
El-Rufai ya bayyana haka ne a sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter da yammacin ranar Laraba.
"Har yanzu ban warke daga cutar covid-19 ba kuma da kaina zan bayyana hakan idan na warke. Ku guji yada labaran karya ko da kuwa kuna son yi," in ji gwamnan.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 1
A ranar Laraba ne, gwamnatin jihar ta ce ta sallami mutum daya cikin mutane shida da suka kamu da cutar korona a jihar.
Gwamna El-Rufai ya sanar da cewa ya kamu da cutar korona ne ranar 28 ga watan Maris.


Sai dai gwamnan ya ce har lokacin bai fara nuna alamun cutar ba amma ya killace kansa.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 2
Sauran su ne:
Abba Kyari - Shugaban Ma'aikata a fadar gwamnatin Najeriya
Bala Muhammad - Gwamnan Bauchi
Seyi Makinde - Gwamnan Oyo
Muhammad Babandede - Shugaban hukumar kula da shige da fice
Sai dai tuni Bala Muhammad, Seyi Makinde da Muhammad Babandede suka bayyana cewa sun warke daga cutar korona.











