KAI TSAYE, Yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya 04/03/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku rahoto kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 4 ga watan Maris 2026.

Taƙaitattu

  • Latsa nan domin shiga zaurenmu na Whattsapp
  • An ɗage taron jana'izar Khamenei
  • Ana zargin mutum 140 sun ɓace bayan nutsewar jirgin ruwan Iran a gabar Sri Lanka
  • 'An yi yunƙurin kai hari da jirgi mara matuƙi kan babban matatar man Saudiyya'
  • Ghana ta rufe ofishin jakadancinta a Tehran saboda rikicin Gabas ta Tsakiya
  • Iran ta kai hari da makamai masu linzami kan sansanin sojin Amurka a Qatar
  • Amurka ta yi iƙirarin kai hare-hare kusan wurare 2000 a Iran tun bayan fara yaƙi
  • Ministan harkokin wajen Iran ya zargi Trump da wargaza tattaunawar sulhu da gangan
  • Iran ta tabbatar da kisan Ali Khamenei a hare-haren Amurka da Isra'ila

Rahoto kai-tsaye

Daga AIsha Babangida da Haruna Kakangi

  1. An kakkaɓo makami mai linzami da ke kan hanyarsa zuwa Turkiyya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran na ci gaba da kai hare-haren makamai masu linzami da jirage marassa matuka kan asashe kamar Turkiyya da Isra'ila da Saudiyya da Kuwait.

    Sai dai na'urorin kare sararin samaniya na ƙungiyar ƙawancen NATO sun kakkaɓo waɗanda ke wucewa ta Syria da Iraqi akan hanyarsu ta zuwa Turkiyya.

    Qatar ta sanar da kakkaɓo makamai masu linzami da ke cin dogon zango guda biyu, sai dai ɗaya daga ciki ya faɗa sansanin soji da ke Al-Udaid.

    An kuma kai hari sansanin sojin Amurka a Hadaddiyar Daular Larabawa, babu wanda ya jikkata ko hasarar rai.

    Tuni Amurka ta rufe ofishin diflomasiyyarta na ƙasashen Saudiyya da Qatar da Lebanon.

  2. ADC ta soki yadda ake tafiyar da shari’o’in Malami da El-Rufai

    ....

    Asalin hoton, Social Media

    Jam'iyyar haɗaka ta ADC ta yi suka kan yadda ake tafiyar da shari'o'in tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai da tsohon ministan shari'a Abubakar Malami tana mai cewa ya kamata a yi amfani da adalci ga kowa ba tare da nuna son rai na siyasa ba.

    A cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na jam'iyyar, Bolaji Abdullahi, ya wallafa a shafin X ranar Talata, ya ce ADC na sa ido kan shari’o’in manyan fitattun ƴan siyasarta.

    Sanarwar ta jaddada cewa babu ɗan ƙasa da ya wuce doka, amma ta nuna damuwa kan abin da ta kira rashin daidaito a yadda ake aiwatar da matakan shari’a da kuma saurin aiwatar da su a kan El-Rufai da Malami.

    Jam'iyar ta ba da misali da wata shari’a da aka yi a kwanan nan da ya shafi tuhumar laifin ƙirƙirar fasfo ba bisa ka’ida ba da cin hanci da ya shafi ƙasashen waje wanda ta ce har a bayar da belin waɗanda ake tuhuma da laifin a wannan shari'ar.

    Amma kuma ba haka ake tafiyar da shari'o'in El-Rufai da Malami ba in ji jam'iyyar.

    Jam'iyyar ta ƙara da cewa, “Abubakar Malami da Nasir El-Rufai ‘yan ƙasa ne kafin su shiga wata jam'iyyar adawa don haka ana ɗaukar su a matsayin waɗanda ba su aikata wani laifi ba a ƙarƙashin Kundin Tsarin Mulki har sai an tabbatar da laifinsu a kotu.”

  3. Ana zargin mutum 140 sun ɓace bayan nutsewar jirgin ruwan Iran a gaɓar Sri Lanka

    ....

    Asalin hoton, Reuters

    Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran mai suna IRIS Dena da safiyar yau.

    Mai magana da yawun rundunar, Budhika Sampath, ya ce ko da yake lamarin ya faru ne a wajen iyakar ruwan ƙasarsu, amma yana cikin yankin da suke da alhakin aikin ceto, don haka wajibi ne su amsa kiran bisa ƙa’idojin ƙasa da ƙasa.

    Ya ce sun tarar da wasu mutane na shawagi a kan ruwa, inda suka ceto su, sannan daga bisani bincike ya nuna cewa mutanen na cikin jirgin ruwan Iran ne.

    A cewarsa, takardun jirgin sun nuna cewa kimanin mutum 180 ne ke cikinsa, sai dai har yanzu ba a tabbatar da ainihin adadin waɗanda suka ɓace ba.

    Tun da fari, sakataren ma’aikatar tsaron ƙasar, Air Vice Marshal Sampath Thuiyakontha, ya shaida wa BBC Sinhala cewa ana kyautata zaton kusan mutum 140 sun ɓace.

    Mai magana da yawun rundunar ya ƙara da cewa a lokacin da suka isa wurin domin aikin ceto, ba su hangi jirgin ba, amma sun ga tabon mai a saman ruwa da kuma kwale-kwalen ceton rai na shawagi.

    Ya zuwa yanzu, rundunar sojin ƙasar ba ta iya tabbatar da abin da ya haddasa nutsewar jirgin ba.

  4. An ji ƙarar fashe-fashe a babban birnin yankin Kurdistan na arewacin Iraq

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    An ji ƙarar jerin manyan fashe-fashe a Erbil, babban birnin yankin Kurdistan na arewacin Iraq.

    Fashe-fashen sun auku ne a kusa da filin jirgin saman Erbil, inda dakarun ƙawancen ƙasashen da Amurka ke jagoranta ke da sansani.

    Rundunar sojin Iraki ta ce ta kakkaɓo wani jirgi marar matuƙi da aka harba zuwa ofishin jakadancin Amurka a Erbil.

    Yankin na cike da ƙungiyoyin Kurdawa, da wasu daga cikinsu ke adawa da gwamnatin Iran.

    Akwai rahotannin cewa shugaba Donald Trump ya yi waya da shugabannin Kurdawa a wannan makon, inda ya shawarce su su tayar da bore don hambarar da gwamnatin Iran din.

  5. Ghana ta rufe ofishin jakadancinta a Tehran saboda rikicin Gabas ta Tsakiya

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Ghana ta sanar da rufe ofishin jakadancinta a Tehran har sai baba ta gani saboda ƙaruwar tashin hankali a yankin Gabas ta Tsakiya.

    Rufewar na zuwa ne sakamakon rikicin da ke ƙara ta’azzara tsakanin Iran da Isra'ila da Amurka.

    Ministan harkokin wajen Ghana, Samuel Okudzeto Ablakwa, ya bayyana cewa an ɗauki matakin ne domin kiyaye lafiyar jakadun Ghana da ke Iran.

    Haka kuma, an yi nasarar kwashe duk ma’aikatan jakadancin daga Tehran.

    A cewarsa, “Ina farin cikin sanar da cewa an yi nasarar kwashe dukkan ma’aikatan ofishin jakadancinmu a Iran cikin ƙoshi lafiya da kwanciyar hankali.”

    Ministan ya jaddada cewa rufe ofishin jakadancin na wucin gadi ne, inda kiyaye lafiyar ma’aikatan Ghana shi ne babban abin da gwamnatin ƙasar ke bai wa fifiko.

    Haka kuma, Ghana ta shawarci ‘yan ƙasarta da su guji yin tafiye-tafiye marasa muhimmanci zuwa wasu sassan Gabas ta Tsakiya, tare da kasancewa suna tuntuɓar jakadancin Ghana a yankin kan duk wani batu.

    Ghana ta kasance tana da alaƙar diflomasiyya da Iran tsawon shekaru, amma hukumomi sun ce matakin rufe ofishin na da nasaba da tsaro.

  6. An ɗage taron jana'izar Khamenei

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Kafar yaɗa labaran Iran sun ce an ɗage taron jana’izar Jagoran addinin ƙasar, Ayatollah Ali Khamenei, wanda aka shirya gudanarwa a daren yau Laraba a Tehran a Masallacin Imam Khomeini.

    Dalilin ɗage taron shi ne “fargabar miliyoyin mutanen da za su halarci taron da kuma buƙatar yin shiri na musamman domin wannan adadi na jama’a da kuma yadda za a tsara taron cikin tsari mai dacewa.

    An kashe jagoran Iran ɗin ne a harin haɗin gwiwar da Amurka da Isra'ila suka kai a ranar Asabar, wanda ya janyo tashin hankali da rikici mai tsanani a yankin Gabas ta Tsakiya.

    Ba a bayyana sabuwar ranar da za a gudanar da taron jana’izar ba.

  7. 'An yi yunƙurin kai hari da jirgi mara matuƙi kan babban matatar man Saudiyya'

    ...

    Asalin hoton, VANTOR

    Ma’aikatar tsaron ƙasar Saudiyya ta ce an yi yunƙurin kai hari da jirgi marar matuƙi kan babban matatar man ƙasar.

    An yi yunkurin kai harin ne kan matatar mai ta Ras Tanura Oil Refinery, wacce ita ce mafi girma a Saudiyya.

    Ma’aikatar ta bayyana cewa “kididdigar farko ta nuna cewa harin haifar da wata illa ba.”

    Iran ta taɓa kai hari kan wannan matatar a baya

  8. Najeriya ta dakatar da ziyarar ibada zuwa Isra’ila saboda rikicin Gabas ta Tsakiya

    ...

    Asalin hoton, Bayo Onanuga/X

    Hukumomi a Najeriya sun dakatar da dukkan ziyarar ibada zuwa ƙasar Isra'ila nan take, sakamakon matsalolin tsaro da ke tasowa daga rikicin da ke ƙara ta’azzara a Gabas ta Tsakiya.

    Sanarwa da hukumar shirya ziyarar ibada ta Kristoci ta fitar ta ce an ɗauki matakin ne domin tabbatar da “lafiya da jin daɗin” matafiya ‘yan Najeriya.

    Dakatarwar ta shafi duk ziyarar ibada da hukumomin gwamnati da na masu zaman kansu ke shiryarwa kuma za ta ci gaba har sai an samu kwanciyar hankali a yankin.

    Dubban ‘yan Najeriya Kiristoci na zuwa Birnin Ƙudus da Bethlehem da Nazareth duk shekara don ziyarar ibada.

    Wannan ziyarar addinin suna da muhimmanci a kalandar addinin Kiristoci ta Najeriya.

    Najeriya, ƙasa mafi yawan mutane a Afirka, na da yawan Kiristoci musamman a kudu, kuma ziyarar ibada zuwa Isra’ila na da matuƙar muhimmanci ga masu bin addinin Krista, inda da yawa ke tattara kuɗi na tsawon shekaru don yin ziyarar.

    Hukumomin Najeriya ba su bayyana lokacin da za a soke dakatarwar ba, amma sun ce suna sa ido sosai kan halin da ake ciki.

    Ba wannan ne karo na farko da ake dakatar da ziyarar ibada ba saboda tsaro.

    A yanzu, an shawarci masu shirin zuwa ziyarar da su jira ƙarin bayani daga hukumomin ƙasar masu ruwa da tsaki.

  9. Kuwait na fuskantar hare-haren makamai masu linzami da jirage marasa matuƙi - Sojoji

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin ƙasar Kuwait ta ce tana fuskantar wani jerin hare-haren makamai masu linzami da kuma jirage marasa matuƙi.

    A wani saƙo da ta wallafa a shafin X, rundunar ta bayyana cewa za ta tunkari makaman tare da kakkaɓe su kafin su kai ga wuraren da aka nufa.

    Wannan na zuwa ne a yayin da rikici ke ƙara ta’azzara a yankin Gabas ta Tsakiya tsakanin Iran da haɗin gwiwar Amurka da Isra'ila.

    A cikin wannan rikici, Iran ta ƙaddamar da harin makamai masu linzami zuwa sansanin sojin Amurka a wasu ƙasashe a yankin Gulf, ciki har da Qatar, a matsayin martani ga hare‑haren da sojojin Amurka da Isra’ila suka kai kan Iran.

    Hukumomin Kuwait sun tabbatar da tsaron fararen hula da ababen more rayuwa.

  10. Spain ta mayar da martani kan barazanar Trump saboda adawarta da harin Iran

    ...

    Asalin hoton, RONALD WITTEK/EPA/Shutterstock

    Firaministan ƙasar Spain, Pedro Sánchez, ya mayar da martani kan barazanar da Donald Trump ya yi na katse hulɗar kasuwanci tsakanin ƙasashen biyu, sakamakon adawar Madrid ga harin da aka kai kan Iran.

    A jawabin da ya gabatar ta gidan talabijin a safiyar Laraba, Sánchez ya jadadda matsayar gwamnatinsa ta hana Amurka amfani da filin jirginta domin kai wa Iran hari.

    "Ba za mu goyi bayan yaƙi ba” in ji firaministan.

    Ya yi kira da kada a maimaita “kurakuran da suka gabata”, yana mai nuni da mamayar da aka yi wa Iraq a 2003, wadda ya ce ba ta cimma manufofinta ba, sai ma ta haifar da rashin tsaro da kuma taɓarɓarewar rayuwar jama’a da dama.

    Sánchez ya ce hare-haren kan Iran na iya haifar da irin wannan tasiri a fannin tattalin arziki ga miliyoyin mutane, kuma gwamnatinsa na duba matakan da za ta ɗauka domin rage illa.

    A ranar da ta gabata, Trump ya sha alwashin “katse duk wata hulɗa” da Spain, tare da kiran ƙasar da suna marar daɗi, bayan da Sánchez ya ƙi amincewa Amurka ta yi amfani da sansanonin sojinta da ke Spain wajen kai hari kan Iran.

    Madrid ta bayyana harin a matsayin “tsoma bakin soja da bai da hujja kuma mai haɗari.”

  11. Ministan harkokin wajen Iran ya zargi Trump da wargaza tattaunawar sulhu da gangan

    ....

    Asalin hoton, Reuters

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya zargi tsohon shugaban Amurka, Donald Trump, da “wargaza tattaunawar sulhu da gangan domin ɓata al'amarin” a wani sabon saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta.

    Araghchi ya ce idan aka ɗauki tattaunawar makaman nukiliya mai sarkakiya tamkar cinikin filaye, tare da yaɗa manyan ƙarya da ke ɓoye gaskiya, ba za a taɓa cimma sakamakon da ake fata ba.

    Ya ƙara da cewa abin da ya biyo baya shi ne wargaza tattaunawar gaba ɗaya ta hanyar amfani da ƙarfi.

    A cewarsa, Trump ya ci amanar diflomasiyya da kuma Amurkawan da suka zaɓe shi.

  12. Amurka ta yi iƙirarin kai hare-hare kusan wurare 2000 a Iran tun bayan fara yaƙi

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Amurka ta yi ikirarin kai hare-hare kusan wurare dubu biyu a Iran tun bayan ƙaddamar da farmakin haɗin gwiwa da Isra'ila.

    Bataliyar rundunar sojin ƙasar a gabas ta tsakiya da ake kira CENTCOM, ta ce ta yi mummunar ɓarna ga garkuwar tsaron samaniyar Iran da kuma nutsar da jiragen ruwan sojin kasar goma sha bakwai.

    Cikin wata sanarwa ta bidiyo, babban kwamandan bataliyar Admiral Brad Cooper, ya ce sojojin Amurka dubu hamsin ne ke yakin.

    Ya ce Iran ta harba makamai masu linzami sama da ɗari biyar, tare da tura jirage marasa matuƙa sama da dubu biyu.

  13. Isra’ila ta gargaɗi mazauna kudancin Beirut su fice

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar Sojin Isra’ila ta fitar da sanarwar gargaɗi ga fararen hula a wasu sassan kudancin birnin Beirut da su fice daga yankin, yayin da musayar wuta tsakaninta da Hezbollah ke ci gaba.

    Rundunar ta ce mazauna yankin Haret Hreik su fice nan take.

    Mai magana da yawun rundunar, Avichay Adraee, ya bayyana cewa an bayar da wannan umarni ne domin kauce wa haɗarin da ka iya tasowa sakamakon hare-haren da ake shirin kaiwa.

  14. Iran ta kai hari kan sansanin sojin Amurka mafi girma a Qatar

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma’aikatar tsaron ƙasar Qatar ta sanar da cewa Iran ta kai hari da makamai masu linzami kan sansanin sojin Amurka a Qatar

    Sanarwar ta ce Gatar ta kaɓo ɗaya daga cikin makaman masu linzami da Iran ɗin ta kai hari da su yayin da kuma ɗayan ya faɗa cikin sansanin sojin Amurka da ke Al Udeid, wanda shi ne mafi girman sansanin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya.

    Hukumomin Qatar sun ce na a samu asarar rayuka ba kuma babu wanda ya jikkata sakamakon harin.

  15. An sanar da lokacin yin jana'izar Ayatollah Khamenei

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    A yau ne ake sa ran fara gudanar da taron jana’izar Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Ayatollah Ali Khamenei, a birnin Tehran kamar yadda kafar yaɗa labaran ƙasar ta sanar.

    Kafar ta ruwaito cewa za a fara taron da misalin ƙarfe 18:30 na agogon GMT, kuma shirye-shiryen za su gudana na tsawon kwanaki uku kafin a yi jerin gwanon jana’iza.

    An kashe Khamenei ne lokacin da Amurka da Isra’ila suka kai hari kan Iran a ranar Asabar, lamarin da ya ƙara tsananta rikicin da ke tsakanin ɓangarorin.

    Jaridar The New York Times ta ambato wasu jami’an Iran na cewa ɗan Khamenei wato Mojtaba Khamenei na daga cikin waɗanda ake ganin suna kan gaba wajen maye gurbinsa.

    Rahoton ya nuna cewa za a iya yanke hukunci kan sabon jagoran tun da safiyar yau.

    A wani ɓangare kuma, Ministan Tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya bayyana cewa duk wanda zai gaji Khamenei kuma ya ci gaba da abin da ya kira shirin rusa Isra’ila ko barazana ga Amurka, tare da danne al’ummar Iran, 'za mu kashe shi.”

  16. Me ya sa Amurka da Isra'ila suka kai wa Iran hari, kuma yaushe yaƙin zai ƙare?

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rikici ya ɓarke a Gabas ta Tsakiya bayan kashe jagoran addinin Iran Ayatollah Ali Khamenei, a wasu hare-haren da Amurka da Isra'ila suka ƙaddamar.

    Bayan harin, shugaban Amurka Donald Trump ya buƙaci al'ummar Iran su tuntsurar da gwamnati.

    A matsayin martani, Iran ta harba makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa a wurare da dama na yankin, kamar ƙasashen Isra'ila da Bahrain da Kuwait da Qatar da Hadaddiyar Daular Larabawa da Jordan da Saudiyya da tsibirin Cyprus, har ma da jiragen dakon man fetur da ke ratsawa ta mashigar Hormuz.

    Haka nan ma ƙungiyar Hezbollah mai samun goyon bayan Iran da ke a Lebanon ta shiga faɗan, inda ta harba rokoki zuwa cikin Isra'ila daga sansanoninta da ke cikin Lebanon.

    Isra'ila ta mayar da martani ta hanyar kai hari kan cibiyoyin Hezbollah a Lebanon.

  17. Yadda kisan Ali Khamenei zai shafi ƴan Shi'a a Najeriya

    ....

    Asalin hoton, JNIM

    Har yanzu duniya na ci gaba da alhinin kisan jagoran addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei, wanda aka kashe a hare-haren da Amurka da Isra'ila suka kai kan Iran.

    Ayatollah mai shekara 86 na da matuƙar tasiri a Iran da ma ƙasashen duniya, musamman tsakanin mabiya aƙidar Shi'a a faɗin duniya

    Tuni dai mabiya ƙungiyar ƴan'uwa Musulmi a Najeriya ta ,yan Shi'a suka shiga jimaminsa ta hanayr gudanar da taron muzaharori da zanga-zangar lumana domin bayyana alhininsu.

    Malam Sidi Mannir Mainasara ɗaya daga cikin manyan almajiran Sheikh Alzakzaky kuma wanda ya san rayuwar Ayatoullah Ali Khamenei, ya bayyana wa BBC yadda mabiya shi'a a faɗin duniya suka ji da rashinsa.

    Ya ce kisan Ayatollah ya ƙara fito da martaba da tasirin aƙidar Shi'a ke da shi a Najeriya.

    ''Za ka sha mamaki idan ka ga yadda mutane suka ajiye bambancin aƙida suka riƙa yi mana ta'aziyyar rasuwarsa'', in ji shi.

    Ya ci gaba da cewa abin ya ba su mamaki, yadda mutuwarsa ta mantar da al'umma bambancin aƙida.

  18. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Laraba.

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.