Neymar zai buga wasan Brazil da Koriya ta Kudu
Kocin Brazil Tite ya tabbatar da cewa Neymar zai buga wasansu da Koriya ta Kudu a zagaye na biyu na gasar cin kofin duniya da Qatar ke daukar bakunci.
Dan wasan mai shekaru 30 bai buga wasanni biyu a jere na Brazil ba, saboda raunin da ya ji a wasansu na farko da Serbiya.
Brazil wacce ake ganin za ta iya lashe gasar ta zama ta farko a rukunin G duk da cewa ta sha kashi a hannun Kamaru a wasansu na karshe na zagayen farko.

Asalin hoton, Getty Images
Tite ya ce "Neymar ya yi atisaye a yau kuma zai iya buga wasanmu na ranar Litinin".
Dan wasan PSG din ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa a yanzu ya samu sauki.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X

Asalin hoton, Getty Images







