Bidiyo: Yadda jirgin kasa na Abuja-Kaduna ya lalace
Jirgin kasa da ke jigila tsakanin Abuja zuwa Kaduna ya lalace a ranar Juma'a.
Jirgin, wanda ya tashi daga tasharsa ta Idu da safiyar Juma'a da ke Abuja, ya tsaya sau biyu kafin ya isa tashar Kubwa.
A tashar ta Kubwa , ya tsaya tsawon fiye da awa daya saboda matsalar da yake fama da ita.
Daga bisani jirgin ya ci gaba da tafiya bayan da aka kawo wani kai aka sanya masa.
Sai dai hukumomi sun bai wa fasinjoji hakuri suna masu cewa injin jirgin ne ya lalace.
Ba wannan ne karon farko da jirgin yake lalacewa ba lamarin da ake dangatakawa da rashin kulawa da shi sosai.