Shugaba Assad ya gana da ministan Iran kan rikicin Syria

Asalin hoton, EPA
Shugaban Syria, Bashar al-Assad ya gana da ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi a Damascus, tare da yin maraba da tallafi domin yaƙi da ƴantawayen da suka ƙawace iko a wasu sassan ƙasarsa.
Mr Assad ya ce taimako daga abokan huɗɗarsa abu ne mai mihimmancin gaske wajen tunkarar abin da ya kira taron ƴan ta'adda.
An daɗe ba a ganin shugaban na Syria, duk da cewa ƴantawaye sun ci gaba da kutsawa arewacin Ƙasar a makon nan.
Rasha ta bai wa Assad tallafin kayan yaƙi ta sama, inda ya riƙa kai wa ƴantawayen hari a Idlib da kuma Hama.
Ma'aikatar tsaron Syria ta ce an kashe gomman mayaƙan ƴantawayen.
Masu sanya ido sun ce an samu rahoton kisan fararen hula a wurare, ciki harda birnin Aleppo da ƴantawayen suka ƙwace.











