Labarin wasanni daga 18 zuwa 30 ga watan Janairun 2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a duniyar wasanni daga Lahadi 18 zuwa 30 ga Janairun 2026

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu

  1. Pedri ya ji rauni a wasan Slavia Praque a Champions League, Barcelona

    Pedri

    Asalin hoton, Getty Images

    Barcelona ta fitar da sabon bayani kan ɗan wasa, Pedri bayan raunin da ya ji a Champions League a wasan da ƙungiyarsa ta je ta ci Slavia Prague 4-2 ranar Laraba.

    Saboda haka Barcelona ta sanar cewar Pedri zai yi jinyar mako huɗu kafin ya koma taka mata leda.

    Hakan babban koma baya ga ne ga koci Hansi Flick a kokarin da yake na gannin Barcelona ta ci gaba da samun nasarori a karawar kakar bana.

    Kawo yanzu Pedri ba zai buga wasan La Liga da Real Oviedo da Elche da Real Mallorca da Girona da kuma Levante.

    Haka kuma ba zai buga wa Barcelona Champions League da za ta kara da Copenhagen ba da kuma zagayen kwata fainal a Copa del Rey da Albacete ba.

  2. , Daga Jaridu

    Bruno Fernandes

    Asalin hoton, Getty Images

    Tottenham na son ta sayi dan wasan West Ham da kuma Netherlands Crysencio Summerville mai shekara 24 kan fam miliyan 25. (Mail)

    Liverpool na zawarcin dan wasan Tottenham da Netherlands Micky van de Ven, mai shekara 24, wanda kawo yanzu bai sa hannu kan sabon kwantaraginsa da Spurs ba. (Mail - subscription required, external)

    Manchester United na shirin fadawa dan wasan tsakiyar Portugal Bruno Fernandes, mai shekara 31, cewa suna son ya ci gaba da taka leda da su na tsawon shekara guda kuma su na son ya yanke shawara kafin gasar cin kofin duniya ta bana. (ESPN)

    Nottingham Forest za ta bar dan wasan Brazil Cuiabano, mai shekara 22, ya tafi wata kungiya a matsayin aro a wannan watan, yayin da take zawarcin dan wasan bayan Liverpool da kuma Girka, Kostas Tsimikas mai shekara 29, wanda a halin yanzu yake zaman aro a Roma (Athletic - subscription required, external)

  3. An tsayar da tattaunawa kan tsawaita yarjejeniyar Wilson a Fulham, Premier League

    Wilson

    Asalin hoton, Getty Images

    Tattaunawar da Harry Wilson ke yi da Fulham kan sabunta sabon kwangila ta tsaya cik, yayin da wasu ƙungiyoyin Premier League ke sha’awar ɗaukar ɗan wasan tawagar Wales.

    Yarjejeniyar Wilson za ta ƙare a ƙarshen kakar bana a Craven Cottage, kuma har yanzu Fulham ba ta cimma matsaya kan tsawaita ta masa ba, duk da cewa ta sanya batun tantance makomarsa mafi fifiko a gareta.

    An fahimci cewa Wilson zai fi so ya samu cikakken bayani kan makomar a wajen koci Marco Silva, wanda shima kwantiraginsa zai ƙare a karshen kakar nan, kafin ya yanke shawara ta ƙarshe kan ko zai ci gaba da taka leda a ƙungiyar.

    Duk da yiwuwar rasa ɗan wasan mai shekaru 28 a ƙarshen kakar bana, Silva ya bayyana cewa babu damar sayar da Wilson a kasuwar saye da sayarwa ta wannan Janairun nan.

    Wilson yana cikin matsayin ɗaya daga cikin ƴan wasan Premier League da ke kan ganiya da taka rawar gani a halin yanzu.

    Ya ci kwallaye shida a wasa 12 a baya-bayan nan a dukkan fafatawa da bayar da biyar aka zura a raga.

    An fahimci cewa ƙungiyoyi da dama na Premier League sun nuna sha’awar ɗaukar Wilson a wannan watan, inda Aston Villa da Brentford da Everton da Crystal Palace ke cikin waɗanda ke sa ido kan halin da yake ciki gabanin ranar ƙarshe ta rufe kasuwa ranar 2 ga watan Fabrairu.

    Ana sa ran wasu ƙungiyoyin Ingila da na Turai za su shiga cikin masu zawarcin ɗan ƙwallon da zarar kwantiraginsa ya kare a karshen kakar bana.

  4. ''Na bukaci ƴan wasa su fita daga fili, saboda ina jin ba a yi mana adalci ba'', Afcon Morocco 2025/26

    Senegal

    Asalin hoton, Getty Images

    Kocin Senegal, Pape Bouna Thiaw, ya ce umarnin da ya bayar na kiran ƴan wasansa su fita daga fili a karawar ƙarshe a gasar cin kofin Afirka da aka buga ranar Lahadi ya samo asali ne yadda ransa ya ɓaci da kuma jin an yi musu rashin adalci.

    A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafin Instagram a ranar Alhamis, Thiaw ya yi ƙoƙarin bayyana dalilin da ya bukaci ƴan wasa su fice daga fili, matakin da mutane da dama suka yi Allah-wadai da shi, kuma wanda ka iya janyo masa hukunci.

    Senegal ta yi zanga-zanga ne bayan da aka bai wa mai masaukin baki Morocco bugun fenariti daf a tashi, bayan da aka duba VAR, inda ’yan wasan Senegal suka bar fili kafin daga bisani su dawo domin ci gaba da fafatawar.

    Morocco ta kasa cin fenaritin, lamarin da ya kai wasan zuwa ƙarin lokaci, inda Senegal ta ci ƙwallo da ya ba ta ɗaukar babban kofin tamaula na Afirka na biyu jimilla cikin gasa uku.

  5. , Daga Jaridu

    Dias

    Asalin hoton, Getty Images

    An yi watsi da tayin da Forest ta yi wa dan wasan Napoli Mathias Olivera , sai dai kawo yanzu tana ci gaba da tattaunawa da kungiyar kan dan wasanta dan kasar Uraguay mai shekara 28. (Tuttomercatoweb - in Italian)

    Celta Vigo ta mika wa Wolves bukatar ba ta aron Fer Lopez , mai shekara 21 , kuma za ta biya dukkan albashin dan wasan tsakiyar Sifaniya da ke cikin tawagar masu shekara kasa da 21.(Sky Sports)

    Real Madrid na son ta dauko dan wasan tsakiyar Portugal Ruben Neves, mai shekara 28, wanda ke son ya bar Al-Hilal, inda Manchester United ita ma ta na son tsohon kyaftin din Wolves . (AS - in Spanish), external

    Dan wasan Chelsea da Ingila Cole Palmer, mai shekara 23, na son ya koma Manchester United, duk da cewa tsohon dan wasan Manchester City nada kwantaragi da Stamford Bridge wanda zai kare a shekarar 2033 . (Express)

    Barcelona na son kyaftin din Manchester City , Bernardo Silva,mai shekara 31, idan kwantaraginsa ya kare a karshen kakar wasa. (Nacional - in Spanish)

  6. Inter na fatan tsawaita tazara tsakaninta da masu biye da ita a Serie A, Gasar Serie A

    Inter

    Asalin hoton, Getty Images

    Inter Milan na sa ran ƙara faɗaɗa tazarar da take tsakaninta da sauran ƙungiyoyi a saman teburin Serie A lokacin da za ta karɓi bakuncin Pisa, wadda ke matsayi na biyu a ƙarshen teburi a karawar da za su yi ranar Juma’a.

    Ana ganin Inter za ta fara wasan ƙarshen mako a matakin mai sauƙi, ranar Lahadi za a buga manyan fafatawa biyu, AC Milan za ta je gidan AS Roma, sannan Juventus ta karɓi bakuncin Napoli.

    Inter na gaba da Milan a kan teburin Serie A da maki uku, yayin da Napoli da kuma Roma mataki na huɗu.

    Juventus tana da tazarar maki 10 tsakani da Inter ta ɗayan teburi, wadda ita kuma take ta biyar, bayan shan kashi da ci 1–0 a hannun Cagliari.

    Ƙungiyar Inter ƙarƙashin jagorancin Cristian Chivu ta sha kashi da ci 3–1 a gida a hannun Arsenal a Champions League ranar Talata, amma duk da haka Inter ta lashe wasa takwas daga cikin tara na baya bayan nan da ta buga a Serie A.

  7. , Tseren motocin Formula 1

    Formula 1

    Asalin hoton, Audi

    Shugaban tawagar McLaren F1, Andrea Stella, ya ce sun aiki mai yawa da ba su taɓa yin irinsa ba, saboda sabbin dokokin da aka kawo a wannan kakar a tseren motocin Formula 1.

    Tawagogin na fuskantar abin da ake kallon shi a matsayin mafi girman sauyin dokoki a tarihin tseren, inda aka gabatar da sabbin motoci da injuna da irin man fetur da ake bukata da tayoyi da za a ke amfani da su daga kakar nan.

    Za a gudanar da atisaye ba tare da ƴan kallo ba a Barcelona mako mai zuwa, kafin a fara gwaje-gwajen kakar a watan gobe a Bahrain.

  8. Djokovic ya kai zagaye na uku a Ausralian Open ranar Alhamis, Australian Open

    Djokovic

    Asalin hoton, Getty Images

    A rana ta biyar ta gasar Australian Open, Novak Djokovic ya doke Francesco Maestrelli kai tsaye ya kai zagaye na uku ranar Alhamis, yayin da yake ci gaba da ƙoƙarin lashe Grand Slam na 25 jimilla.

    Iga Swiatek, wadda ke neman cika burinta na lashe dukkan manyan gasar Grand Slam a wasanninta na tennis, ta doke Marie Bouzkova da ci 6–2, 6–3 ta kuma kai zagaye na uku.

    Itama Naomi Osaka ta doke Sorana Cirstea ta kuma kai zagayen gaba.

    Haka kuma Madison Keys da Amanda Anisimova da Jannik Sinner duk sun kai bante a wasannin da ake yi a birnin Melbourne.

  9. Watakila Bergvall na Tottenham ya yi jinyar wata uku, Tottenham

    Tottenham

    Asalin hoton, Getty Images

    Tottenham na jiran cikakken sakamakon bincike kan raunin idon sawun kafa da Lucas Bergvall ya ji yayin da ake fargabar cewa zai iya jinya har tsawon watanni uku.

    Dan ƙwallon tawagar Sweden ya ji raunin ne a wasan da suka doke Borussia Dortmund da ci 2–0 a gasar Champions League a daren Talata, kuma an sauya shi a zagaye na biyu bayan da ya yi ƙoƙarin ci gaba da fafatawar duk da raunin da ya ji.

    Yanzu ana sa ran Bergvall mai shekaru 19 ba zai samu damar buga wasu wasanni ba nan gaba, labari da zai zama babban koma baya ga koci Thomas Frank.

    Likitocin ƙungiyar na ci gaba da tantance girman raunin, dalilin da ya sa har yanzu Tottenham ba ta kai ga fayyace kwanakin da zai yi jinya ba.

    Ana cewa jinyar wata uku ita ce mafi muni da Bergvall zai yi, bisa gwaje-gwajen farko da aka yi masa.

    Bergvall ya koma Tottenham a watan Fabrairun 2024 kuma ya buga wasa 26 ga ƙungiyar arewacin London a wannan kakar.

    Tottenham na matsayi na 14 a teburin Premier League, wadda ke fuskantar kalubale tun bayan da Frank ya karɓi aiki tun kan fara kakar bana.

    Kocin ɗan Denmark yana fama da jerin ƴan masu yawa da ke jinya, daga ciki har James Maddison da Rodrigo Bentancur da Mohammed Kudus da Dejan Kulusevski da kuma Ben Davies.

    Ana sa ran Richarlison zai dawo buga wasanni, bayan jinyar mako shida, sai dai shima Palhinha na jinya a sabon raunin da ya ji.

  10. , Daga Jaridu

    Frank Onyeka

    Asalin hoton, Getty Images

    Sheffield United da Coventry da Valencia na zawarcin danwasan Brentford da Nigeria Frank Onyeka, mai shekara 28 (Standard, external)

    Aston Villa na zawarcin danwasan tsakiyar AC Milan da Ingila Ruben Loftus-Cheek, mai shekara 29, domin ta inganta tsakiyarta. Wannan nada alaka da mumunan raunin da dan wasanta kuma ɗan Faransa Boubacar Kamara mai shekara 26 ya ji. (Telegraph - subscription required)

    An kuma yi wa Manchester United tayin Loftus-Cheek inda suka tattauna domin samun bayyanai akan shi .(Talksport)

    Villa ta tuntubi Fenerbahce kan danwasan gaba, Youssef En-Nesyri a cikin sa'oi 24 da suka gabata kuma dan wasan Morokon mai shekara 28 zai yanke shawara game da makomarsa nan bada jimawa ba inda Napoli da Juventus duk suna sha'awarsa. (Fabrizio Romano, external)

  11. Ƙwallo ɗaya Haaland ya ci a wasa takwas baya, ko yana bukatr hutu?, Manchester United

    Haaland

    Asalin hoton, Getty Images

    Erling Haaland ya fara kakar wasa da bana da kwarin gwiwa, amma kuma bayan da wasanni ke nisa ya ci karo da koma baya.

    Duk da cewa ɗan wasan Manchester City da tawagar Norway ya ci kwallaye 39 a wasa 36 a kasarsa da ƙungiyarsa a wannan kakar, ya shiga wani yanayi na kasa zura ƙwallo a raga inda ya ci ɗaya tak a wasa takwas a baya-bayan nan.

    Hakan ya zo daidai da lokacin da ƙungiyar da Pep Guardiola ke jan ragama ta fara ja da baya a gasar Premier League, haka kuma City ta yi rashin nasara 3-1 a gidan Bodo a Champions League ranar Talata.

    City ba ta yi nasara ba a Premier League tun da aka shiga shekarar 2026, wadda ta raba maki da Sunderland da Chelsea da Brighton daga baya Manchester United ta doke ta 2-0.

    Guardiola ya danganta shan kashin da suka yi a wasan hamayya a Old Trafford ranar Asabar da ta gabata da rashin kuzari.

    Shin ɗan wasan mai shekaru 25 ya buga wasanni da yawa a wannan kakar ne, kuma ya dace kocin nasa ya ɗan ba shi hutu ne?

  12. An yi ƴan wasan Senegal alkawarin kuɗi da gidaje a bakin teku, Afcon Morocco 2025/26

    Afcon

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban ƙasar Senegal, Bassirou Diomaye Faye, ya yi alkawarin ba da kuɗi sama da dalar Amurka 130,000, tare da filaye a bakin teku, ga kowane ɗan wasan tawagar kasar a matakin ladan lashe Afcon ranar Lahadi a Morocco.

    Ya bayyana hakan ne a wani biki da aka gudanar a babban birnin ƙasar, Dakar, inda dubban magoya baya suka yi ta murna suka cika tituna domin tarbar zakarun kofin Afirka, Lions of Teranga, bayan dawowarsu gida.

    Senegal ta doke mai masaukin baki, Morocco, da ci 1–0 bayan ƙarin lokaci a karawar da aka samu cece-kuce a ƙarshen mintuna 90, inda aka yanke hukuncin ba da bugun fanareti, lamarin da ya sa suka fice daga filin wasa kafin daga bisani a ci gaba da karawar.

  13. Fifa Club Wprld na mata na fuskantar Suka, Fifa Club World Cup na mata

    Arsenal

    Asalin hoton, Getty Images

    Shirya gudanar da gasar Fifa Club World Cup ta mata da aka shirya yi yana fuskantar suka mai tsanani, inda gasar ƙwallon kafa ta mata ta Ingila (WSL) ta bayyana cewa hakan na iya zama babbar barazana.

    Hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya, Fifa, ta sanar da cewa za a gudanar da gasar a karon farko, wadda aka tsara yi kamar yadda tsarin Club World Cup ta maza da za a fara daga 5 zuwa 30 ga Janairu, 2028.

    Wannan lokaci zai faɗa ne a tsakiyar kakar wasan WSL ta 2027–28, lamarin da ya haifar da korafi daga sauran manyan gasar cikin gida da ta Turai.

    Gasar za ta ƙunshi ƙungiyoyi 16 daga sassa daban-daban na duniya, ciki har da guda shida daga Turai.

    A Ingila zai haɗa da Arsenal, wadda ke rike da kofin Champions League a halin yanzu, da kuma Chelsea mai yiyuwa ta shiga bisa la’akari da yawan maki a wasannin da take bugawa wato (co-efficients) na yanzu.

    Gasar Champions Cup, wadda za ta haɗa zakarun nahiyoyi daga sassa daban-daban na duniya ciki har da Arsenal, za a gudanar da ita mako mai zuwa a London, daga 28 ga Janairu zuwa 1 ga Fabrairu.

    Jami’an WSL sun ce gasar Club World Cup da aka tsara za ta tilasta a sake tsara jadawalin wasanni har zuwa mako biyar a WSL, wanda zai iya haifar da cunkoson wasanni da zai iya shafar lafiyar ƴan wasa.

    Saboda haka sun rubuta wasiƙa zuwa Fifa domin bayyana damuwarsu, kuma za su gana da jami’an a London a lokacin gasar Champions Cup domin tattauna wannan batu.

  14. , Daga Jaridu

    Lamens

    Asalin hoton, Getty Images

    Inter Milan na zawarcin golan Aston Villa Emiliano Martinez, mai shekara 33, amma dan wasan na Argentina dole ne ya amince da rage masa albashi don kulla yarjejeniya a bazara mai zuwa.(Sky Sports)

    Bournemouth ba za ta amince da duk wani tayi da za a yi wa Marcos Senesi, mai shekara 28, a cikin wannan watan ba, inda Chelsea da Juventus da kuma Barcelona ke cikin masu zawarcinsa dan wasan na Argentina . (Talksport)

    Ana ganin Kocin Coventry Frank Lampard shi ne zai maye kocin Crystal PalaceI da kuma kocin Getafe Jose Bordalas da kuma na Rayo Vallecano, Inigo Perez. (Talksport)

    Sunderland ba ta da niyyar sayar da dan wasan tsakiya na DR Congo Noah Sadiki, mai shekara 21, ga Manchester United, amma a shirye take ta saurari tayin da ake yi wa 'yan wasa irinsu golan Ingila Anthony Patterson, mai shekara 25, da tsohon dan wasan Ingila na 'yan kasa da shekara 20 Dan Neil, mai shekara 24.(Sun)

  15. Alcaraz ya kai da zagayen gaba a Australian Open da ƙyar, Australian Open

    Alcaraz

    Asalin hoton, Getty Images

    Carlos Alcaraz ya kai zagaye na uku bayan fuskantar kalubale a hannun Yannick Hanfmann a Australian Open.

    Haka itama, Aryna Sabalenka ta sha tata ɓurza kafin ta kai zagayen gaba a wasannin da ake bugawa a birnin Melbourne.

    An ɗan samu tsaiko a wasan, Alexander Zverev sakamakon zubar ruwan sama daga baya ya kai zagaye na uku.

    Tuni Coco Gauff ta yi saurin doke Olga Danilovic ta kai zagayen gaba, sauran da suka yi kwazo irin nata sun haɗa da Jasmine Paolini da kuma Mirra Andreeva.

    Alcaraz ya yi nasara a kan Hanfmann da ci 7-6(4), 6-3, 6-2 a filin wasa na Rod Laver.

  16. Ƴan Bournemouth sun roƙi a sayo musu ƴan wasa - Iraola, Bournemouth

    Iraola

    Asalin hoton, Getty Images

    Andoni Iraola ya ce ƴan wasansa na Bournemouth suna ta roƙon a kawo sabbin ƴan ƙwallo domin ƙara ƙarfin ƙungiyar, saboda fuskantar sauran kalubalen da ke gabansu.

    Bournemouth na fama da karancin ƴan wasa musamman a bangaren kai hari bayan da ta sayar da babban mai zura kwallaye, Antoine Semenyo, zuwa Manchester City, sannan kuma Justin Kluivert na jinyar raunin gwiwa.

    Haka kuma, Julio Soler da David Brooks da Enes Unal da ƴan wasan da suka dade suna jinya Tyler Adams da Ben Gannon-Doak ba su buga wasan Premier League da suka tashi 1-1 da Brighton a daren Litinin ba, yayin da mai cin ƙwallo Marcus Tavernier ya fita daga karawar saboda raunin da ya ji.

  17. Ƴan wasan City za su biya tikitin magoya baya da suka je Bodo, Manchester City

    City

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƴan wasan Manchester City za su mayar da kuɗin tikiti ga magoya baya 374 da suka je Norway a wasan da suka yi rashin nasarar da ci 3-1 a hannun Bodo/Glimt a gasar Champions League ranar Talata.

    Farashin tikitin kallon wasan ya kai kusan fam 25, ƴan wasan City za su haɗa jimillar kuɗi fam 9,357, domin mayar da kuɗin ga magoya bayan domin rage musu raɗaɗin doguwar tafiyar zuwa yankin Arctic Circle, domin mara baya ga ƙungiyar da suke kauna.

    Da suke magana a madadin ƴan wasan, ƙungiyar kyaftin City wato Bernardo Silva da Ruben Dias da Rodri da Erling Haaland sun ce: “Magoya bayanmu sune komai a gare mu.”

  18. Wasannin da za a buga a Champions League ranar Laraba, Champions League

    Champions League

    Asalin hoton, Getty Images

    • Atalanta da Ath Bilbao
    • B Munich da Union St Gilloise
    • Chelsea da Pafos
    • Galatasaray da Atl Madrid
    • Juventus da Benfica
    • Marseille da Liverpool
    • Newcastle da PSV Eindhoven
    • Qarabag da Frankfurt
    • Slavia Prague da Barcelona
  19. , Daga Jaridu

    Tuchel

    Asalin hoton, Getty Images

    Aston Villa ta nuna sha'awar sayen dan wasan Crystal Palace da Faransa Jean-Philippe Mateta, mai shekara 28, yayin da Eagles na neman dan wasan Villa dan kasar Ivory Coast Evann Guessand, mai shekara 24.(Athletic - subscription required)

    Har ila yau, Villa na kara matsa kaimi wajen daukar dan wasan gaba na kungiyar, Roma Tammy Abraham, wanda a halin yanzu yake zaman aro a Besiktas, inda jami'an kungiyar suka kalli wasan da dan Ingilan mai shekaru 28 a duniya ya yi a Istanbul ranar Litinin.(Sky Sports)

    Ajax ta nemi a bata aron Manuel Ugarte, mai shekara 24, yayin da take neman dan wasan tsakiya amma Manchester United ba ta son ta bada da dan wasan dan kasar Uruguay.(Athletic - subscription required)

    Kocin Borussia Dortmund Niko Kovac ya fito a matsayin sabon suna a cikin jerin sunayen 'yan wasan Manchester United da zasu zama kocinsu na gaba amma babban kocin Ingila Thomas Tuchel da Roberto de Zerbi na Marseille sun kasance a kan gaba .Open in Google Tran (Mirror)

  20. Marseille ta cimma yarjejeniyar ɗaukar aron Nwaneri daga Arsenal, Arsenal

    Nwaneri

    Asalin hoton, Getty Images

    Marseille ta cimma yarjejeniya da Arsenal domin ɗaukar aron Ethan Nwaneri har zuwa ƙarshen kakar bana.

    A baya BBC ta ruwaito cewa ba a sa ran Nwaneri zai je wasannin aro a wannan kakar, inda a baya Arsenal da matashin mai shekara 18 ke tunanin idan ya ci gaba da taka leda a Gunners zai kara samun gogewa.

    Sai dai damar buga ƙwallo a wata ƙasa a wata gasar daban da samun damar buga wasanni akai-akai, wani abu ne da ya ja hankalin ɗan wasan.

    Ɗan ƙwallon tawagar Ingila ta matasa ƴan kasa da shekara 21, ya buga wasa 12 kacal a dukkan fafatawa a Arsenal a wannan kakar, inda ya fara wasa huɗu amma babu ko ɗaya a Premier League, kuma ya ci ƙwallo ɗaya a Carabao Cup.

    Nwaneri ya sanya hannu kan kwantiragin ci gaba da taka leda a Arsenal a lokacin bazara wanda zai kai kare a karshen kakar 2030.