OPEC za ta ƙara yawan man da take haƙowa saboda yaƙin Iran

Asalin hoton, Getty Images
Ƙungiyar ƙasashe masu arzikin man fetur ta OPEC ta sanar da aniyar ƙara yawan man da take haƙowa sakamakon yaƙin Isra'ila da Iran da kuma Amurka.
Ƙungiyar - wadda ta ƙunshi manyan ƙasashe masu arzikin man fetur, kamar Saudiyya da ƙasashen yankin Gulf da ke cikin fargabar harin ramuwar gayyar Iran - ta amince ta ƙara yawan man da take haƙowa da ganga 260,0000 a kowace rana.
Ƙungiyar na son maye gurbin man da aka rasa a kasuwar mai ta duniya, daga ƙasashen Amurka da Kanada da kuma Brazil.
Ana sa ran yaƙin ya kawo tsaikon tono mai a Iran, lamarin da ka iya tayar da farashin man.


















