Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 23/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 23 ga watan Fabrairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Abdullahi Bello Diginza

  1. Matakan da gwamnatin Tinubu ke ɗauka wajen daƙile matsalar tsaro ba sa aiki - Amnesty

    AMNESTY INTERNATIONAL

    Asalin hoton, AMNESTY INTERNATIONAL

    Ƙungiyar Amnesty International ta ce yadda garkuwa da mutane domin karɓar kuɗin fansa da kashe-kashe ke ƙaruwa a arewacin Najeriya na jefa mutane cikin matsananciyar rashin tsaro da firgici.

    Ƙungiyar ta ce matsalar ta ƙara fito da rashin ƙoƙarin gwamnati, wadda a cewarta ta gaza wajen kara rayuwa da dukiyar ƴan Najeriya.

    A wata sanarwa da ƙungiyar ta Amnesty International ta fitar a ranar Litinin, ta ce: "yadda hare-haren Lakurawa da Mamuda da Boko Haram da ƴanbindiga ke sake zama ɗanye sun nuna cewa matakan da gwamnatin Tinubu ke ɗauka wajen daƙile matsalar tsaro ba sa aiki," kamar yadda sanarwar ta bayyana.

    Bola Tinubu ya zama shugaban Najeriya ne a watan Mayun shekarar 2023, "da alƙawarin tabbatar da tsaro. Amma maimakon haka, sai matsalar ta ƙara ruruwa, inda hukumomi suka gaza kare rayuka da mutuncin dubban ƴan Najeriya," in sanarwar.

    Sanarwar ta ƙara da cewa dokokin Najeriya tana nauyi a wuyanta na kare rayuka da dukiyar al'umma, "tare da tabbatar da kamawa tare da hukunta waɗanda suke aikata waɗannan laifuka, sannan a tabbatar an yi wa waɗanda aka illata adalci."

  2. El-Rufai ya maka ICPC a kotu

    Nasir El-Rufai/X

    Asalin hoton, Nasir El-Rufai/X

    Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya maka hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ICPC a kotu, kamar yadda mai magana da yawunsa, Muyiwa Adekeye ya wallafa a shafinsa na X.

    El-Rufai ya kamata ICPC ne a babbar kotun tarayya da ke Abuja, inda ya buƙaci kotun ta ayyana takardar izinin shiga bincike a gidansa a matsayin mara ingaci, sannan ta bayyana cewa an tauye masa haƙƙi.

    Haka kuma ya buƙaci kotun ta tursasa hukumar ta mayar masa da kayayyakin da ake kwasa a gidan nasa, sannan ta hana hukumar amfani da su a gaba.

    Rahotanni dai na nuna cewa El-Rufai na tsare ne a hannun hukumar ta ICPC, sannan kuma sun je gidansa domin bincike a cigaba da gudanar da binciken da take kan zarginsa da aikata laifuka.

    Tun da farko EFCC ce ta fara tsare El-rufai, sannan daga bisani aka samu labarin ya koma hannun ICPC, inda ita ma take gudanar da nata binciken dabam.

  3. An kashe mana mutum biyar a Filato - Ƙungiyar Gan-Allah

    Shau

    Asalin hoton, Getty Images

    A daidai lokacin da ake cigaba da jimamin mutuwar aƙalla mutum bakwai da ake zargin wasu ƴanbindiga da kashewa, shugaban ƙungiyar Fulani ta Gan-Allah ya ce su ma a ɓangarensu an kashe makiyaya aƙalla mutum biyar.

    Shugaban ƙungiyar, Garba Abdullahi ya ce an kashe musu mutum uku, "a lokacin da suke dawowa daga wajen tafsiri, aka tare su aka kashe a Barikin Ladi, sannan akwai wasu da aka kashe a ƙaramar hukumar Riyom, mun yi wa biyu jana'iza, ɗaya kuma ba mu gan shi ba," in ji shi.

    Ya yi zargin cewa rashin adalci ne yake hana ruwa gudu domin tabbatar a zama lafiya a jihar, "domin bai kamata a ce a duk lokacin da aka samu asara ba, sai a ce Fulani ne za su biya diyya."

    Yanzu dai al’ummar ƙananan hukumomin Barkin Ladi da Riyom na jihar ta Filato na ci gaba da zaman ɗar-ɗar bayan hare-hare waɗanda suke da alaka da ƙabilanci.

    Tun da farko, rahotanni sun nuna cewa ƴanbindiga su kai hari inda ake zaton aƙalla mutum bakwai ne suka mutu yayin da wasu uku suka jikkata a harin da aka kai wa al’ummar Ratatis da ke Dorowa Babuje a ƙaramar hukumar Barkin Ladi da ke jihar Filato.

    Shugaban matasan yankin, Zain Kefas ya shaida wa BBC cewa an tare wasu matasa ne a ranar Asabar aka kashe su, sannan suka samu labarin ƴanbindiga sun harba kusan mutum 10, inda ya yi zargin cewa Fulani ne makiyaya suka kai harin.

    Kamar sauran jihohi masu maƙwaftaka irin su Benue da Nasarawa, Jihar Filato ta daɗe tana fama da rikici mai nasaba da ƙabilanci tsakanin makiyaya - waɗanda akasarinsu ƴan ƙabilar Fulani ne - da kuma manoma - waɗanda su kuma akasarinsu ƴan ƙananan ƙabilu ne mazauna yankin.

  4. Ana ci gaba da matsa wa DSS lamba kan ta saki Walida

    DSS

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani lauya mai rajin kare haƙƙin bil’adama a Najeriya, Barista Hamza Nuhu Dantani ya rubuta wata wasiƙa zuwa ga Hukumar tsaron farin kaya DSS ta ƙasar, inda yake nuna damuwa dangane da yadda ya ce hukumar ta ɗauki batun zargin sacewa, da kuma yin lalata da wata mace, Walida Abdulhadi, da ake zargin ɗaya daga cikin jami’anta Ifeanyi Onyewuenyi da yi.

    A cikin wasiƙar, lauyan ya saka ayar tambayar kan dalilan ƙin miƙa yarinyar ga iyayenta da kuma abin da ya kira ƙoƙarin kare jami'in da hukumar ke yi.

    Batun matashiyar na ci gaba da ɗaukar hankali a Najeriya tun bayan da wasu gungun lauyoyi suka shigar da ƙara suna zargin wani jam'in hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (DSS) da laifin "sacewa da yin lalata da kuma sauya wa wata yarinya mai suna Walida Abdulhadi addini."

    Rahotanni sun bayyana cewa jami'in na hukumar DSS ne ya tuntuɓi iyayen yarinyar, inda ya shaida musu cewa yana riƙe da ita, kuma har ta haifa masa ɗa, a wata unguwa da ke Abuja, babban birnin Najeriya.

    A cikin koken da Barista Nuhu ya rubuta, ya ce "An ɗauke yarinyar ne a lokacin da take aji biyu a babbar sakandare, kuma mahaifinta ya sha nanata cewa ƙaramar yarinya ce a lokacin da ta ɓace."

    Lauyan ya buƙaci a miƙa ta zuwa ga iyayenta, inda ya ƙara da cewa babu dokar da ta ba DSS damar ci gaba da riƙe matashiyar. "Don haka ina kira da a saki Walida ba tare da ɓata lokaci ba, sannan wasu daban su gudanar da bincken ba DSS ba."

    Haka kuma wasu ƙungiyoyin rajin kare haƙƙin ɗan'adam sun kai nasu koken, inda suka buƙaci DSS ta gaggauta sakin Walida, domin a cewarsu tana ƴar shekara 16 ne ya tafi da ita.

    Ƙungiyoyin, waɗanda suka rubuta koken a ƙarƙashin Gamji Lawchain a madadin mahaifin yarinyar, sun yi zargin cewa jam'in ya sace ta, sannan ya yi lalata da ita, tare da tilasta mata komawa addinin Kirista.

    Daga cikin ƙungiyoyin akwai International Human Rights Commission Relief Fund Trust (IHRC-RFT) da Women Voices and Accountability da Muslim Rights Concern (MURIC) da sauransu.

  5. Tsohon shugaban ƙasar Philippines na fuskantar shari’a kan laifukan cin zarafin bil’adama

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Masu gabatar da ƙara a kotun hukunta manyan laifuka ta duniya na ci gaba da gabatar da bayanai kan tuhumar da suke yi wa tsohon shugaban Philippines, Rodrigo Duterte.

    Ana zarginsa da aikata laifukan cin zarafin bil’adama a yayin yaƙin da gwamnatinsa ta yi da masu safarar miyagun ƙwayoyi.

    Ɗaya daga cikin masu gabatar da ƙarar ya shaida wa kotun cewa Duterte ya riƙa bayar da umurnin kashe mutane da kansa, har ma yana zaɓen waɗanda za a kashe.

    Bayan lauyoyin masu ƙara sun kammala gabatar da bayanansu, kotun za ta yanke hukunci kan ko akwai isassun shaidu da za su ba ta damar sauraron shari’ar gaba ɗaya.

    A ɓangaren kariya kuwa, lauyan tsohon shugaban ya shaida wa kotun cewa wanda yake karewa bai aikata wani laifi ba.

  6. Chadi ta rufe kan iyakarta da Sudan

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙasar Chadi ta rufe kan iyakarta da Sudan har zuwa wani lokaci.

    Sanarwar da gwamnatin ƙasar ta fitar ta ce ta ɗauki wannan mataki ne domin dakatar da kutsen da ƙungiyoyi da ke ɗauke da makamai na Sudan ke yi a ƙasar.

    A cikin sanarwar, ministan harkokin sadarwa na Chadi, ya ce ya na son ya daƙile duk wani haɗarin bazuwar rikicin zuwa ƙasarsa

    A ranar Asabar da ta gabata an samu ɓarkewar faɗa a garin Al- Tina da ke kan iyaka, tsakanin mayaƙan RSF da wasu mayaƙa da ke goyon bayan sojojin Sudan.

  7. Ƴanbindiga sun kashe mutum bakwai a Filato

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni na ci gaba da fitowa gama da wani hari da ƴanbindiga suka kai inda ake zaton aƙalla mutum bakwai ne suka mutu yayin da wasu uku suka jikkata a harin da aka kai wa al’ummar Ratatis da ke Dorowa Babuje a ƙaramar hukumar Barkin Ladi da ke jihar Filato.

    Shugabannin al’umma sun shaida wa BBC cewa harin ya faru ne da yammacin Lahadi, lamarin da ya jefa mazauna yankin cikin firgici yayin da mutane suka tsere zuwa dazuka domin neman mafaka.

    Sabon harin ya ƙara shiga jerin hare-haren da suka jima suna faruwa a Najeriya, inda hare-haren makamai ke yawaita a arewa da tsakiyar ƙasar tsawon kusan shekara goma.

    Rikice-rikicen sun jawo asarar rayuka da raba dubban mutane da muhallansu, tare da ƙara matsin lamba ga gwamnati ta ɗauki matakan gaggawa.

    Masu nazarin tsaro sun daɗe suna gargaɗin cewa rashin tsaro na lalata hanyoyin samun abinci da tattalin arziki, musamman a yankunan karkara da noma ne ginshiƙi cin su.

    Harin na Lahadi ya zo ne a daidai lokacin da gwamnatin ƙasar ta bayyana cewa wasu daga cikin masu kai hare-haren da ake kama wa ba ’yan ƙasar ba ne.

    Da yake jawabi a wani taron coci a Abuja, sakataren gwamnatin tarayya George Akume ya ce bayanan cewa wasu daga cikin waɗanda ake tsare da su ba sa jin Turanci sosai, Hausa kaɗan suke fahimta, kuma galibi suna magana da Faransanci, abin da jami’an tsaro suka ɗauka a matsayin alamar cewa sun shigo daga ƙasar waje.

    Gwamnatin ta ce tana ɗaukar matakai domin shawo kan matsalolin tsaro, inda Akume ya amince cewa rashin tsaro na daga cikin manyan ƙalubalen da ’yan ƙasar ke fuskanta, amma ya jaddada cewa ana ci gaba da aiki tukuru domin magance su.

  8. Nijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyu

    Shugaban Jamhuriyar Nijar Abdourahamane Tiani

    Asalin hoton, Presidence De La Republique Du Niger

    Bayanan hoto, Shugaban Jamhuriyar Nijar Abdourahamane Tiani

    Jamhuriyar Nijar ta amince da kundin ayyukan Ƙungiyar Kasashen Sahel (AES) na shekara ta biyu wadda ta haɗa da Mali da Burkina Faso, kafin taron ministoci da za a gudanar a Ouagadougou daga 24 zuwa 26 ga watan Fabrairu, kamar yadda jaridar gwamnati ta ANP ta ruwaito a ranar 21 ga Fabrairu.

    Firaminista Ali Mahamane Lamine Zeine ya gana da ministoci da mambobin kwamitin ƙasa na AES a ranar 21 ga Fabrairu domin daidaita matsayi kafin taron yankin.

    Mataimakiyar Shugabar kwamitin, Bayard Mariama Gamatie, ta ce Burkina Faso ta raba wani kundin aiki, wanda Nijar ta gyara bisa ginshiƙai uku da suka haɗa da tsaro da diflomasiyya, ci gaban ƙasa, da tsaro da kare iyaka.

    "An amince da kundin gaba ɗaya, dangane da shawarwarin gyare-gyaren Nijar," in ji Gamatie.

    Rahoton ya nuna cewa ministocin Nijar sun duba kundin sun kuma yi gyare-gyare da sake fasalta wasu abubuwa, sannan sun bayar da shawarwari don taron ƙwararru da zai biyo baya.

    An kafa AES a shekarar 2023, bayan da ƙasashen uku suka janye daga Ƙungiyar ECOWAS, domin tsara manufofi na tsaro da diflomasiyya, da ci gaban ƙasa tsakanin ƙasashen Sahel.

  9. Gwamnan Sokoto ya buƙaci masu hali su riƙa ciyar da masu azumi

    Sokoto

    Asalin hoton, Office of the Press Secretary, Government House Sokoto

    Gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu ya yi kira ga masu hannau da shuni a jihar su taimaka wajen cikyar da mabuƙa a faɗin jihar.

    Gwamnan ya yi kirane ne a lokacin da ya kai ziyara wata cibiyar da gwamnatinsa ke ciyar da masu azumi.

    Ya ce gwamnatinsa na bayar da tallafin abincin buɗe-baki ga masu azumi a jihar, wanda ya ce za a riƙa bai wa aƙalla masu azumi 34,000 a kullum.

    A lokacin ziyarar, gwamnan ya ziyarci cibiyoyin da ke titin Clapperton da Lodge Road da Gidan Dallatu da asibitin ƙwararru da yankin Madunka, inda ya yaba da ingancin abincin da ake rabawa ga mutane.

    “Na yaba da ingancin abincin, da kuma irin yadda ake zuba wa mutane isasshen abinci. Duk wuraren da na ziyarta, na gamsu da aikin da suke yi,” in ji gwamnan.

    Gwamnan ya ƙara da cewa an samu ci gaba a irin ingancin abincin a bana, idan aka kwatanta da irin abincin da aka raba a shekarar da ta gabata.

    Ya kuma yaba da ƙoƙarin masu aikin ciyarwar, waɗanda ya ce suna matuƙar ƙoƙari. “Mun ƙirƙiri ciyarwar nan ne domin sauƙaƙa wa marasa ƙarfi domin su samu sauƙin yin buɗe-baki. Don haka ina kira ga kwamitin abincin su ƙara ƙaimi,” in ji shi.

    Ahmad Aliyu ya yi alƙawarin ci gaba da ba ciyarwar azumi muhimmanci a gwamnatinsa.

    Ya ce gwamnatin jihar ta ware naira biliyan 1 domin ciyarwar azumin bana, inda ya ce kullum za a ciyar da mutum 34,000 ne.

  10. Atiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasa

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, kuma jigo a jam’iyyar haɗaka ta ADC ya nuna damuwa kan ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a da aka samu a zaɓen ƙananan hukumomin Abuja na ranar Asabar, yana mai zargin cewa hakan na nuna yadda ake yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasa a ƙarƙashin shugabancin Bola Tinubu.

    A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, ya wallafa a shafinsa na X, ya bayyana cewa yawan jama’ar da suka fito zaɓen Abuja bai kai kashi 20 cikin 100 ba wata alama da ke nuna halin da dimokuraɗiyyar Najeriya ke ciki a yanzu.

    Ya ce "Ƙarancin masu kaɗa kuri'a da aka samu a babban birnin ƙasar ba abin mamaki ba ne, illa sakamakon yanayin siyasa da ya ce ya cika da rashin haƙuri da tsoratarwa da kuma rage ƙarfin muryoyin adawa."

    A cewarsa, "idan ’yan ƙasa suka daina yarda cewa ƙuri’unsu na da tasiri, dimokuraɗiyya ya fara mutuwa."

    Ya ƙara da cewa "abin da ake gani ba sakamakon rashin sha’awar zaɓe kaɗai ba ne, illa sakamakon shugabanci da ke takura tsarin dimokuraɗiyya."

    Ya ce "dimokuraɗiyya ba za ta cika ba idan babu ƙarfi a ɓangaren adawa, babu gasa ta gaskiya a siyasa, kuma babu amincewar jama’a."

  11. Habasha za ta faɗaɗa ƙarfin sojinta yayin da zaman ɗar-ɗar ke ƙaruwa a yanki

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Firaministan Habasha, Abiy Ahmed, ya sanar da shirin faɗaɗa ƙarfin rundunar sojin ƙasar tare da ƙirƙirar wata runduna ta musamman da za ta kare yankunan gaɓar teku da kuma yaƙi da ta’addanci da fashin teku a yankin ƙahon Afrika.

    Ya bayyana hakan ne a wani taro da aka gudanar a Hawassa City International Stadium ranar 22 ga Fabrairu, 2026 domin bikin cika shekaru 65 da kafuwar rundunar musamman ta ƙasar.

    Abiy Ahmed ya jaddada cewa shirye-shiryen soja ba domin tayar da faɗa ba ne, sai dai domin tabbatar da zaman lafiya a yankin.

    Ya ce ƙasar za ta taimaka wajen kare zaman lafiya daga gabɓar tekun Somaliya har zuwa tashar jiragen ruwa ta Massawa a Eritrea.

    Firaministan ya kuma bayyana cewa rundunar za ta taimaka wajen kare gabar tekun yankin tare da ƙarfafa yaƙi da fashin teku da ta’addanci.

    Ya ƙara da cewa Habasha ta bunƙasa ƙarfinta na soja, ciki har da amfani da jirage marasa matuƙa domin leƙen asiri da kai hare-hare.

    Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da rikici ke ƙaruwa tsakanin Habasha da Eritrea sakamakon yunƙurin Addis Ababa na samun damar shiga teku da ikon mallaka.

  12. AU ta yi allawadai da kisan fiye da mutum 50 a Zamfara

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar Tarayyar Afirka ta yi allawadai da abin da ta kira munanan hare-haren ƴan bindiga da aka kai a jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya, inda aka kashe fiye da fararen hula 50 tare da sace mata da yara da dama.

    A sanarwar da shugaban hukumar ƙungiyar, Mahmoud Ali Youssouf ya fitar a ranar Lahadi, ya bayyana harin a matsayin babban take hakkin bil’adama da kuma barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

    Rahotanni sun nuna cewa harin ya faru ne a ƙauyen Dutsin Dan Ajiya da ke ƙaramar hukumar Anka, inda ‘yan bindiga sama da 150 suka mamaye garin da yamma a kan babura

    Sun kuma tare hanyoyin shiga da fita domin hana mutane tserewa sannan suka riƙa harbi ba tare da kakkautawa ba kafin nan suka ƙone gidaje.

    Majiyoyin yankin sun ce maharan sun shafe sa’o’i suna kai farmaki tun daga daren Alhamis har zuwa safiyar Juma’a.

    Wasu mazauna sun bayyana cewa sun sanar da jami’an tsaro tun da suka hango maharan na tahowa, amma ba su samu ɗauki cikin lokaci ba.

    Ƙungiyar ta nuna cikakken goyon baya ga gwamnatin Nijeriya da al’ummarta, tare da jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu da kuma yi wa waɗanda suka jikkata fatan samun sauƙi cikin gaggawa.

    Ta kuma bukaci a saki mutanen da aka sace nan take ba tare da wani sharaɗi ba, tare da kira ga ƙarin haɗin gwiwar tsaro domin kare jama’a da hana sake aukuwar irin waɗannan hare-hare.

    Zuwa yanzu dai gwamnatin Nijeriya ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.

  13. PDP za ta kai APC kotu kan zaɓen Abuja

    ....

    Asalin hoton, PDP

    Jam’iyyar PDP ta sanar da kafa wata ƙungiyar lauyoyi ta musamman domin ƙalubalantar sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi da aka gudanar a yankunan babban birnin tarayya, Abuja.

    Matakin na zuwa ne bayan sakamakon da INEC ta bayyana ya nuna cewa ‘yan takarar APC sun lashe kujerun shugabancin ƙananan hukumomi biyar cikin shida.

    APC ta yi nasara a ƙananan hukumomin Abaji da ƙaramar hukumar birni wato AMAC da Bwari Kwali da Kuje, yayin da PDP ta samu nasara a Gwagwalada kaɗai. An gudanar da zaɓen ne domin cike kujerun shugabanni shida da na kansiloli 62.

    Jam’iyyar ta ce zaɓen ya gudana cikin yanayi na rashin fitowar masu kaɗa ƙuri’a da kuma rahotannin sayen ƙuri’u.

    A sanarwar da sakataren yaɗa labaranta na ƙasa, Ini Ememobong, ya fitar, jam’iyyar ta taya waɗanda suka yi nasara murna amma ta jaddada cewa akwai kura-kurai a sakamakon.

    Ta bayyana cewa ƙungiyar lauyoyinta za ta kasance ƙarƙashin jagorancin mai ba ta shawara kan harkokin shari’a na ƙasa, Shafi Bara’u, tare da kira ga duk ‘yan takarar da ke da ƙorafi su gaggauta gabatar da su domin ɗaukar mataki.

  14. EFCC ta kama mutum 20 bisa zargin laifukan zaɓe a Abuja

    ...

    Asalin hoton, efcc

    Hukumar EFCC ta sanar da kama mutum 20 da ake zargi da aikata laifukan zaɓe yayin zaɓen ƙananan hukumomin babban birnin tarayya, Abuja da aka gudanar a ranar 21 ga Fabrairu, 2026.

    Ta ce an kama su ne a wurare daban daban saboda zarge zargen sayen ƙuri’u da sayar da ƙuri’u da kuma hana jami’ai aiki, inda aka gano kuɗi har Naira miliyan 17,218,700.

    A cikin sanarwar da mai magana da yawun hukumar, Dele Oyewale, ya fitar, an ce an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin da Naira miliyan 13,500,000 a cikin mota da aka ajiye kusa da rumfar zaɓe a yankin Kwali.

    Sanarwar ta ƙara da cewa an kama mutane biyu a Abaji, tara a Gwagwalada, huɗu a Kuje, sannan sauran huɗun a Kwali.

    Hukumar ta ce za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.

    Hukumar INEC ce ta gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi da kansiloli a dukkan yankuna shida na FCT.

    Haka kuma an gudanar da zaɓukan cike gurbi a mazaɓun Ahoada East II da Khana II na Jihar Rivers.

    An kuma gudanar da zaɓe a mazaɓun Kano Municipal da Ungogo na Jihar Kano.

    EFCC ta jaddada cewa za ta ci gaba da sa ido domin tabbatar da gaskiya da adalci a dukkan matakan zaɓe.

  15. Zelensky ya zargi Putin da ƙaddamar da yaƙin duniya na uku

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban ƙasar Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya bayyana wa BBC cewa takwaransa na Rasha, Vladimir Putin, ya riga ya ƙaddamar da abin da ya kira yaƙin duniya na uku, yana mai cewa abin da ya dace a yi masa shi ne ƙara matsin lambar soji da ta tattalin arziki.

    A hirar da aka yi da shi gabanin cika shekaru huɗu da mamayar da Moscow ta kai wa ƙasarsa, Zelensky ya zargi Putin da yunƙurin kafa sabon tsarin rayuwa a duniya.

    Ya kuma yi gargaɗi cewa hare-haren ba za su tsaya kan ƙasarsa kaɗai ba idan ba a dakatar da shi ba.

    Ya ce ƙasarsa ba za ta yi rashin nasara ba domin tana yaƙi ne don kare ‘yancin cin gashin kanta. A cewarsa, duk da tsawon lokacin rikicin, har yanzu Ukraine na tsaye daram kuma ba ta rasa ikon mallakar kanta ba.

    Shugaban ya ƙara da cewa rikicin ya jawo asarar rayukan dubban daruruwan mutane, ciki har da fararen hula, tare da haddasa matsaloli ga tattalin arzikin duniya.

    Ya jaddada cewa dole ne ƙasashen duniya su ƙara haɗin kai wajen ɗaukar matakan da za su hana rikicin ya ƙara faɗaɗa, yana mai cewa matsin lamba na haɗin gwiwa shi ne hanya mafi inganci ta dakile barazanar.

  16. Mece ce makomar ‘dalaget’ bayan sauya dokar zaɓen Najeriya?

    ...

    Asalin hoton, BolaTinubu/X

    A makon da ya gabata ne, Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sanya hannu kan sabuwar dokar zaɓen ƙasar ta 2026, da aka yi wa gyaran fuska.

    Shugaban ya sa hannu kan dokar – wadda ta ƙunshi ƙa'idojin yin zaɓukan tarayya da jihohi da kuma ƙananan hukumomin yankin birnin tarayya.

    A lokacin sanya hannu kan dokar, Tinubu ya ce "babu batun siyasa a cikin wannan gyare-gyare, abu ne na tsari, ƙoƙari ne na cike giɓi da ƙarfafa tsari da kuma samar da tsaftatacciyar hanya ga masu tsarawa da kuma masu yin zaɓuka."

    Shugaban na Najeriya ya sanya hannu kan dokar ne bayan hargitsin da aka samu a zaurukan majalisar tarayyar ƙasar da ma zanga-zangar da ƙungiyoyin fararen hula suka yi game da gyaran da aka yi wa dokar.

    Ɗaya daga cikin manyan gyare-gyaren da aka yi wa dokokin zaɓen shi ne hanyoyin da jam'iyyu ke bi wajen zaɓen mutanen da za su tsaya musu takara a kujeru daban-daban, wato zabukan fitar da gwani.

  17. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Litinin daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.