Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 21/01/2026

Wannan shafi ne da kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 21 ga watan Janairun 2026.

Taƙaitattu

  • Latsa nan domin shiga zaurenmu na Whattsapp
  • An fitar da sunayen mutanen da aka sace a Kaduna
  • An yanke wa tsohon firaminstan Koriya ta Kudu hukuncin ɗaurin shekara 23
  • Sojojin sun gano makeken kabarin ƴan Boko Haram a yankin Timbuktu
  • Al-Shabaab ta ƙwace muhimmin tsibirin Kudhaa a Somaliya
  • Mutum 39 sun mutu a Khartoum na Sudan sakamakon zazzaɓin Denge
  • Trump na kan hanyar zuwa Switzerland bayan samun matsalar jirgi
  • Kotu ta yanke wa mutumin da ya harbi tsohon firaminstan Japan hukuncin rai da rai
  • Yadda ƴansanda suka yi amai suka lashe kan sace mutane a Kaduna

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida, Haruna Kakangi da Ahmad Bawage

  1. Isra'ila ta jinkirta rusa filin ƙwallon ƙafa na yaran Falasdinawa

    ...

    Isra'ila ta ɗage rusa filin wata ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta yaran Falasɗinawa a birnin Bethlehem, da ke yankin gaɓar yamma da kogin Jordan da ta mamaye.

    Isra'ila ta ce an gina filin na Aida Youth Centre ba tare da izinin da ya dace ba.

    Ta ce rushe filin ya zame dole saboda dalilai na tsaro.

    Da alama dai wani yunƙurin da ƙasashen duniya ke yi na ceto filin, ciki har da takardar koke mai dauke da sa hannun sama da mutane dubu ɗari biyar,ya tilastawa hukumomi sake tunani.

    Sai dai ƙungiyar ta ce har yanzu ba ta samu wata sanarwa a hukumance ba.

    A cikin sanarwar ta baya-bayan nan, rundunar sojin Isra'ila ta sake nanata iƙirarinta na cewa filin wasan kwallon kafar na haifar da matsalar tsaro.

  2. Japan ta sake buɗe tashar nukiliya mafi girma a duniya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙasar Japan ta sake buɗe tashar nukiliya mafi girma a duniya kusan shekaru 15 bayan wani bala'i a tashar nukiliya ta Fukushima ya tilastawa ƙasar rufe dukkan cibiyoyin nukiliyarta.

    Reactor no.6 a masana'antar Kashiwazaki-Kariwa dake arewa maso yammacin Tokyo ya fara aiki ne ranar Laraba.

    An jinkirta fara aikinsa da kwana ɗaya saboda ɗan tangarɗar na'ura da aka samu amma ana sa ran fara aiki gadan-gadan a wata mai zuwa.

    Wannan shi ne kashi na baya-bayan nan a sake fara aikin makamashin nukiliya na Japan,

    Kasar wadda ta dogara kacokan kan shigo da makamashi daga waje, ta kasance cikin sahun farko na kasashen da suka fara amfani da makamashin nukiliya .

    Amma an yi watsi da waɗannan buƙatun a cikin 2011 sakamakon girgizar ƙasa mafi ƙarfi da aka taɓa gani a Japan, da ya janyo narkewar injinan da ke tashar nukiliya ta Fukushima Daiichi.

  3. Ba zan yarda da matsin lambar da Trump ke yi kan Greenland ba - Starmer

    ...

    Firaministan Burtaniya, Sir Keir Starmer ya ce "ba zai yi kasa a gwiwa ba" ga matsin lamba daga Donald Trump kan makomar Greenland, bayan da shugaban Amurka ya soki yarjejeniyar tsibirin Chagos da Burtaniya ta ƙulla.

    Da yake jawabi a filin tambayoyin firaminista, Sir Keir ya ce shugaban na Amurka ya soki yarjejeniyar ta Chagos bayan da a baya ya ce ya goyi bayanta "saboda ya ƙara matsin lamba a kaina da Biritaniya dangane da matsayata kan makomar Greenland".

    A ranar Talata, Trump ya kira yarjejeniyar Burtaniya ta bai wa Mauritius tsibirin Chagos tare da ba da hayar wani muhimmin sansanin soji a matsayin "wani babban wauta".

    Ya yi barazanar sanya haraji kan ƙasashen Turai da ke adawa da buƙatarsa ​​ta karɓe iko da Greenland.

    Sir Keir ya shaida wa ƴan majalisar cewa "makomar Greenland ta mutanen Greenland ne da kuma Masarautar Denmark kaɗai" - kuma ya ce zai karbi baƙuncin firaministan Denmark Mette Frederiksen a Downing Street ranar Alhamis.

    Shugabar jam'iyyar adawa Kemi Badenoch ta ce ta goyi bayan matsayin Firaminista kan Greenland - amma ta amince da Trump kan yarjejeniyar tsibiran Chagos.

    Ta buƙaci Firaministan da ya "yi watsi da wannan mummunar yarjejeniyar tare da sanya kuɗaɗen a ɓangaren rundunar sojojin mu".

  4. Netanyahu ya amince ya shiga kwamitin zaman lafiya na Trump

    Trump da Natanyahu

    Asalin hoton, Reuters

    Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya amsa gayyatar da aka yi masa na shiga cikin kwamitin zaman lafiya na Gaza ƙarƙashin jagorancin shugaban Amurka Donald Trump.

    Wata Sanarwa da ofishinsa ya fitar ta ce Netanyahu zai zama mamba a kwamitin "wanda zai ƙunshi shugabannin duniya".

    Tun da farko dai ana tunanin kwamitin na da nufin taimakawa wajen kawo ƙarshen yaƙin shekaru biyu tsakanin Isra'ila da Hamas a Gaza da kuma sa ido kan sake gina ƙasar.

    Amma yarjejeniyar da ta gabatar ba ta ambaci yankin Falasdinu ba kuma da alama an tsara kwamoitin ne don maye gurbin ayyukan Majalisar Dinkin Duniya.

    Tuni dai ƙasashen Bahrain da Masar da Hadaddiyar Daular Larabawa suka kuma amince da shiga kwamitin kamar yadda Albaniya da Armeniya da Azerbaijan da Belarus da Hungary da Kazakhstan da Morocco da Turkiyya da Vietnam suka bayyan ta su amincewar da shiga kwamitin.

    Trump zai zama shugaban kwamitin kuma shi ne zai kasance a matsayin wakilin Amurka.

    Wani jami'in Amurka ya ce Trump na iya riƙe shugabancin har sai ya yi murabus", amma shugaban Amurka na gaba zai iya zaɓar sabon wakili.

  5. Ƙungiyar ƴan tawaye ta yi iƙirarin ƙwace wani muhimmin gari a Sudan ta Kudu

    South Sudan

    Asalin hoton, AFP

    Ƙungiyar masu dauke da makamai da ke adawa da gwamnati a Sudan ta Kudu, SPLA, ta ce dakarunta sun ƙwace wani muhimmin birni a wani hari da ta kai da nufin ƙara nausawa cikin babban birnin ƙasar Juba.

    Ta ce ta kama Panyume a wani hari da suka kai da hantsin jiya Talata, inda suka ƙwace makamai da motoci masu sulke na dakarun gwamnati.

    Kafafen yaɗa labarai na cikin gida sun ce mahukunta a lardin Morobo sun musanta rahotannin da ƙungiyar ke fitarwa, inda suka ce dakarun gwamnati sun daƙile harin.

    Birnin Panyume na wata muhimmiyar mashiga zuwa Juba, lamarin da ke sanya fargabar cewa akwai yiwuwar yaƙin da ake yi na kusantar babban birnin.

  6. FRSC ta kama wani jami’in bogi da ke ƙwace babura a Kano

    ...

    Asalin hoton, FRSC

    Hukumar kiyaye haɗura ta Najeriya (FRSC), reshen Jihar Kano ta kama wani mutum da ake zargi da ƙwace babura a sassa daban-daban na jihar, yayin da yake yin sojan gona da jami’in FRSC.

    An tabbatar da kama mutumin a wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Abdullahi Labaran, ya fitar a ranar Laraba.

    A cewar sanarwar, wanda ake zargin mai suna Abdullahi Ali, ɗan ƙauyen Bela a ƙaramar hukumar Ungoggo da ke jihar Kano inda aka kama shi a ranar 19 ga Janairun 2026, bayan samun korafe-korafe da dama daga jama’a.

    Labaran ya ce korafe-korafen sun shafi mutanen da ke yin sojan gona da jami’an FRSC domin ƙwace babura ba bisa ka’ida ba, suna fakewa da cewa suna aikin sintiri ne.

    Binciken farko ya nuna cewa wanda ake zargin yana amfani da ƙarfi wajen ƙwace babura yayin da yake yin sojan gona, inda ake zargin an sace wasu daga cikin baburan da aka ƙwace.

    Ya ƙara da cewa an samu lasisin tuki na bogi a hannun wanda ake zargin lokacin da aka kama shi, lamarin da ke nuna amfani da shaidar ƙarya wajen aikata laifin.

  7. Dole Turai ta tsaya da ƙafarta a fannin tsaro - von der Leyen

    von der Leyen

    Asalin hoton, EPA

    Shugabar hukumar gudanarwa tarayyar Turai, Ursula von der Leyen, ta ce wajibi ne Nahiyar Turai ta gaggauta tashi tsaye wajen tsayawa da ƙafafunta a fannin tsaro, a yayin da ake samun ƙaruwar taɓarɓarewar alamurra a duniya.

    Ta faɗawa majalisar Turai cewa wannan taɓarɓarewar bin dokar a duniya ba lalacewa ta ɗan lokaci ba ne, wani abu ne da zai iya daɗewa, kuma ya kamata Turai ta yi watsi da al'adarta ta yin taka tsan-tsan.

    Kalaman na Miss von der Leyen na zuwa ne a yayin da alaƙa tsakanin su da Amurka ke ƙara taɓarɓarewa saboda barazanarsa ta ƙwace yankin Greenland.

    Ta ce Turai a shirye ta ce ta mayar da martani cikin gaggawa, inda ta yi gargadin cewa lalacewar alaƙarsu na ƙara ƙarfafa abokan adawarsu.

  8. Zelensky ba zai halarci taron tartalin arziki a Davos ba

    Zelensky

    Asalin hoton, EPA

    Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya tabbatar da cewa ba zai halarci taron ƙungiyar tattalin arzikin duniya da ake yi a Davos ba.

    Ya ce ya yi hakan ne saboda matsalar makamashi da ake fuskanta a Ukraine, da kuma jinkirin da ake samu wajen amincewa da shirin da ake yi wa ƙasarsa na bayan yaƙi.

    Ya sa ran zuwa yanzu an kammala kashi casain na yarjejeniyar kawo ƙarshen yakinsu da Rasha, sai dai ya ce ganin cewa Trump ya mayar da hankali kan Greenland, hakan na nufin har yanzu akwai sauran aiki.

    Wakilin BBC ya ce shugaban Ukraine ɗin da takwarorinsa na Turai sun sa ran a kammala yarjejeniyar saura sanya hannu, ko kuma ma a ci gaba da tattaunawa kanta a Davos.

    Sai dai a jawabin da ya yi a Davos, shugaban ƙungiyar ƙawancen tsaro ta NATO, Mark Rutte, ya dage cewa batun yaƙin Ukraine ne ya fi zama mafi muhimmanci a gare su ba batun Greenland ba.

  9. Mali ta ce samar da man fetur na ƙaruwa a ƙasar

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar kula da sha'anin kasuwanci ta Mali (DGCC) ta bayyana cewa samar da man fetur a ƙasar na ƙaruwa inda manyan motocin tanki ke isa tashoshin mai a ƙasa da sa'o'i 48, kamar yadda jaridar Malijet mai zaman kanta ta ruwaito.

    Hukumar ta ce man da aka samar a ranar 19 ga Janairu ya isa ya biya buƙatun ƙasa na tsawon makonni da dama.

    "Hukumar na kira ga al’umma su ci gaba da amfani da man fetur yadda aka saba, kuma su guji sayen fiye da kima."

    Hukumar na aiki tare da ‘yansandan ƙasar wajen tabbatar da tsaro yayin jigilar man fetur inda jami’ai suka ce dawowar jigilar tankokin a hankali na tabbatar da cewa samun man fetur ya na komawa yadda yake a duk fadin ƙasar.

    Wannan sanarwa ta biyo bayan makonni na samun ƙarancin man fetur sakamakon toshe hanyoyi da kungiyar JNIM da ke da alaƙa da al-Qa’ida ta yi tun farkon Satumba 2025, wanda ya rufe hanyoyin isar da man fetur zuwa Bamako da sauran birane.

  10. Chadi ta ƙulla yarjejeniyar haɗin gwiwar soji da Belarus

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙasashen Chadi da Belarus sun rattaɓa hannu kan wata yarjejeniya ta bunkasa kawancen soji.

    Ministan abubuwan more rayuwa na Chadi Amir Idriss Kourda, a madadin ministan tsaron kasar da kuma ministan masana’antun soji na Belarus Dmitry Pantus ne suka kammala yarjejeniyar a birnin N’Djamena, a jiya Talata.

    Ta wannan yarjejeniyar, ƙasashen biyu za suyi amfani da ƙwarewar sojin juna da musayar fasaha da horo, sannan su haɓaka ayyuka tare a fannin masana’antar soji.

    Hukumar tsaron Chadi ta bayyana cewa wannan yarjejeniyar za ta zamanatar da ƙasar wajen tunkarar tsaro da inganta ƙarfin tsaron ƙasar, musamman a daidai lokacin da ƙasar ke fuskantar barazanar tsaro daga Boko Haram da sauran ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai da masu tayar da hankali a al’umma.

    A shekarar 2024, hukumomin Chadi sun umarci sojojin Amurka da Faransa sun janye daga ƙasar abin da ya ƙara jawo damuwa kan tasirin yaƙi da ta’addanci a yankin Sahel mai fama da tashe-tashen hankula.

  11. Hotunan cocin C and S da ke Kurmin Wali a Kaduna inda aka sace mutane

    ...

    Ga wasu hotuna da ke nuna cocin Cherubim and Seraphim da ke Kurmin Wali, wani a ƙauye a Kaduna da ke fama da matsalar tsaro inda aka sace mutane a lokacin da suke ibada.

    An sace mutum 92 daga wannan cocin yayin da masu bauta ke gudanar da taron addini.

    Wannan lamari ya zama wani abin damuwa cikin jerin sace-sacen da ke ci gaba da afkuwa a yankunan Arewa maso Yammacin Najeriya, wanda ya janyo fargaba ga jama'a.

    Mutum 170 ne gaba ɗaya aka sace daga ƙauyen inda aka yi musu ƙofar raggo tare da kora su zuwa daji amma daga baya al'ummar sun bayyana cewa mutane 10 sun samu tserewa daga hannun ƴan bindigar.

    A yau Talata ne al'ummar yankin suka fitar da sunayen waɗanda aka sace

    ...
    ...
    ..
    ...
    ...
  12. An yanke wa tsohon firaminstan Koriya ta Kudu hukuncin ɗaurin shekara 23

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Wata kotu a Seoul, babban birnin Koriya ta Kudu, ta yanke wa tsohon firaministan ƙasar, Han Duck-Soo, hukuncin zaman gidan yari na shekaru 23 saboda hannu a ayyukan tayar da tarzoma.

    Laifukan da ake tuhumarsa da su sun shafi ƙoƙarinsa na ayyana dokar soji a lokacin mulkin tsohon shugaban ƙasa Yoon Suk Yeol a Disamban 2024, wanda bai samu tasiri ba.

    Wani alkali ya bayyana cewa an gurfanar da tsohon firaminstan ne saboda ya gaza gudanar da taron yan majalisa da ya kamata a yi kafin a ayyana dokar soji karkashin tsarin mulki.

    Han Duck-Soo ya rike mukamin shugaban riƙo na Koriya ta Kudu na tsawon makonni bayan tsige Yoon.

  13. An fitar da sunayen mutanen da aka sace a Kaduna

    ...

    An fitar da sunayen mutum 170 da aka sace a ƙauyen Kurmin Wali a jihar Kaduna, bayan rahotanni sun bayyana cewa wasu mahara sun kai hari a ƙauyen da ke fama da matsalar tsaro.

    A ranar Litinin ne rahotanni suka bayyana cewa wasu mahara sun kai farmaki a ƙauyen sa'ilin da al'umma ke ibada a coci-coci, inda suka yi musu ƙofar raggo tare da kora su zuwa daji.

    Daga baya al'ummar sun bayyana cewa mutane 10 sun samu tserewa daga hannun ƴan bindigar.

    A jiya Talata shalkwatar rundunar ƴansanda ta Najeriya ta tabbatar da faruwar al'amarin bayan musantawa da ta yi tun farko.

    Sanarwar da ta samu sa hannun mai magana da yawun rundunar ta ƙasa, Benjamin Hundeyin ta ce binciken da sashin tattara bayanan sirri na rundunar ya gudanar ya tabbatar masu cewa an yi garkuwa da mutanen.

    Jerin sunayen waɗanda aka sacen da al'ummar suka fitar ya ƙunshi mutum 177 da kuma shekarunsu.

    Al'ummar sun bayyana cewa sun tattara sunayen ne daga coci-cocin da aka shiga aka aka kwashe masu ibadar a ranar Lahadi.

  14. Sojojin sun gano makeken kabarin ƴan Boko Haram a yankin Timbuktu

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa sojojin haɗin gwiwarta na Operation Haɗin kai da JTF sun gano wani makeken kabarin wasu mayaƙan Boko Haram a yankin Timbuktu, wanda aka ƙiyasta yana ɗauke da gawarwaki guda 20 da aka kashe.

    Sanarwar rundunar ta ce wannan kabarin an gano shi ne yayin da sojoji ke ci gaba da ayyukan samame da ragargazar ‘yanbindiga a yankin, musamman a wani tashar jiragen ruwa da ke kilomita 6 arewa da Chilaria.

    A yayin samamen, sojojin sun gamu da motoci biyu masu ɗauke da abubuwan fashewa.

    Duk da cewa sun samu nasarar kawar da ɗaya daga cikin motocin, ɗayan motar ta fashe, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar wasu daga cikin sojojin da kuma raunata wasu.

    An gaggauta ɗaukar waɗanda suka ji rauni zuwa asibiti domin samun kulawa, yayin da rundunar ke ci gaba da ayyukanta na tabbatar da tsaro a yankin.

  15. Al-Shabaab ta ƙwace muhimmin tsibirin Kudhaa a Somaliya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar Al-Shabaab ta sake ƙwace iko da garin tsibirin Kudhaa da ke yankin Lower Juba a Somaliya, bayan kazamin fada da ta yi da dakarun tsaron Jubaland.

    Garin Kudhaa, wanda a baya ke ɗauke da sansanin soji da sojojin Kenya ke amfani da shi yana kan gaɓar teku a kudu maso yammacin birnin Kismayo, kimanin kilomita 100 daga can.

    Harin ya faru ne da sassafe kafin wayewar gari.

    Wani jami’in dakarun Jubaland ya shaida wa BBC cewa ‘yan Al-Shabaab sun karƙe ikon yankin da misalin karfe 2 na dare, bayan da dakarun gwamnati suka janye daga garin.

    Daga bisani, ƙugiyar ta bayyana cewa ita ce ta kwace tsibirin Kudhaa.

    A baya, Al-Shabaab na amfani da tsibirin a matsayin muhimmin wajen fitar da gawayi zuwa ƙasashen Gabas ta Tsakiya, wanda ke daga cikin manyan hanyoyin samun kudin shiga na kungiyar.

    An kwace Kudhaa daga hannun Al-Shabaab a shekarar 2014 ta hannun dakarun Somaliya tare da goyon bayan sojojin Kenya.

    Sai dai tun daga lokacin, yankin ya ci gaba da zama mai fama da rikici, inda kungiyar ke kai hare-hare akai-akai domin sake karbe iko da garin.

    Har zuwa yanzu, gwamnatin Somaliya da gwamnatin Jubaland ba su fitar da wata sanarwa ba dangane da abin da ya faru a Kudhaa.

  16. Mutum 39 sun mutu a Khartoum na Sudan sakamakon zazzaɓin Denge

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Likitoci a Sudan na ƙoƙarin yaƙi da yaɗuwar zazzaɓin Denge wanda sauro ke yaɗawa.

    A Khartoum, cutar ta kashe mutum 39 yayin da wasu ɗaruruwa suka kamu da ita.

    Asibitocin birnin da dama ba su aiki saboda yadda yaƙi tsakanin dakarun gwamnati da mayaƙan RSF ya ɗaiɗaita su.

    Ƙungiyar likitocin ƙasar ta ce mata da ƙananan yara na cikin waɗanda suka fi kamuwa da zazzaɓin na Denge a ƙasar.

  17. An yi jana'izar babban limamin Ilorin Imam Muhammad Bashir

    Imam Muhammad Bashir

    Asalin hoton, Imam Muhammad Bashir

    Bayanan hoto, Imam Muhammad Bashir

    An gudanar da jana’izar marigayi Limamin Ilorin, Sheikh Muhammad Bashir Solih, wanda ya rasu a ranar Litinin, a unguwar Egbejila da ke jihar.

    Abin da ya fi ɗaukar hankali a jana’izar shi ne cewa an binne gawarsa a cikin wani ɗaki a gidansa.

    Bayan rasuwarsa, an kai gawarsa zuwa Muhammad Soliu Islamic Center, Egbejila, Ilorin, inda aka binne shi a gidansa na asali.

    Kafin jana’izar, mutane da dama sun taru a fadar Sarkin Ilorin, Alhaji Ibrahim Sulu-Gambari, domin yin addu’o’i na ƙarshe da girmamawa ga marigayin.

    Limami Sheikh Abdullahi Abdulhameed ne ya jagoranci sallar jana’izar.

    An binne shi da misalin karfe 12 na rana yayin da kuma mutane suka je bakin kabarinsa suna masa addu’a.

    Imam Muhammad Bashir

    Jana’izar ta samu halartar dimbin mutane.

    An haifi marigayin a ranar 7 ga Yuli, 1951, kuma a ranar 15 ga Oktoba, 1983, aka naɗa shi limami na goma sha biyu na Ilorin.

    Imam Muhammad Bashir
  18. Sifaniya ta dakatar da jigilar jiragen ƙasa a Catalonia bayan mummunan hatsari

    ...

    Asalin hoton, Catalonian fire service

    Hukumomi a Sifaniya sun dakatar da duk wata jigilar jiragen ƙasa a yankin Catalonia, bayan mummunan hatsarin da ya sake aukuwa a jiya Talata.

    Hatsarin shi ne na biyu a cikin kwanaki uku a ƙasar, kuma hukumomi sun yi amanna cewa rashin yanayi mai kyau ke haifar da shi.

    Mutum 37 ne suka samu rauni, huɗu daga cikin su kuma suna cikin mawuyacin hali, yayin da direban jirgin ya mutu.

    Yankin Catalonia na cikin wuraren da gurɓatar yanayi ta yi ƙamari a Sifaniya a ƴan kwanakin nan.

  19. Trump na kan hanyar zuwa Switzerland bayan samun matsalar jirgi

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaba Donald Trump na kan hanyarsa ta zuwa ƙasar Switzerland domin halartar taron ƙoli na tattalin arziƙin duniya da ke gudana a birnin Davos, bayan ya samu jinkiri sakamakon wata matsala da ta taso a na’urar jirginsa na Air Force One.

    Lamarin ya saka Trump hawa wani jirgi na daban domin kammala tafiyarsa zuwa Davos.

    A bana, taron ya fi karkata ga muhawara kan ƙoƙarin shugaba Trump na ganin yankin Greenland ya koma wani ɓangare na Amurka, matakin da shugabannin Turai ke nuna adawa da shi.

    Yayin ganawarsa da manema labarai, an tambayi shugaba Trump game da shirinsa a kan Greenland, inda ya kaɗa baki ya ce: “Za ku sani nan gaba kaɗan.”

    A jiya Talata ne shugabannin Turai da ke halartar taron Davos suka sake jaddada matsayinsu na adawa da wannan buri na Amurka.

    Sai dai Trump ya nace cewa haɗa Greenland da Amurka zai taimaka wajen ƙarfafa tsaron ƙasashen yammacin duniya.

  20. An yanke wa mutumin da ya harbe tsohon firaiministan Japan ɗaurin rai-da-rai

    ...

    Asalin hoton, Reuters

    Wata kotu a Japan ta yanke hukuncin ɗaurin rai-da-rai kan Tesuya Yamagami, mutumin da ya harbi tsohon firaiministan ƙasar Shinzo Abe a wajen wani gangamin siyasa kusan shekaru huɗu da suka gabata.

    Yamagami ya amsa laifin yunƙurin kisan kai a watan Oktoban bara, lokacin da aka fara shari'ar, amma ya musanta wasu zarge-zargen da aka yi masa.

    Tsohon firaiminstan ya mutu bayan harbin da aka yi masa yana tsakiyar jawabi a lokacin taron.

    Masu gabatar da ƙara sun ce Yamagami ya daɗe yana riƙe da tsananin ƙiyayyar tsohon firaiministan, lamarin da ya sa ya harbe shi.

    ...

    Asalin hoton, Getty Images