Hare-haren Isra'ila sun kashe aƙalla mutum 50 a Lebanon

Asalin hoton, Reuters
Jami'ai a Lebanun sun ce sama da mutum 50 hare-haren makamai masu linzami da Isra'ila ta harba Tandem ya yi ajali a ƙasar.
Sama da mutum 150 sun jikkata, a abin da suka kira ramuwar gayya kan goyon bayan Iran da kasar ke yi.
Isra'ila ta ce ta kai harin ne a birnin Beirut, kan duk wani mai alaƙa da ƙungiyar Hezbollah da mayaƙan jihadi na Falasɗinu.
Rahotanni sun bayyana cewa dubban farar hula ne suka sterewa muhallansu a kudancin Lebanun. Tun da fari ƙungiyar Hezbollah ta kai hare-haren makaman roƙa da jirage marasa matuƙa zuwa Isra'ila bayan kisan jagoran addinin Iran Ayatullah Ali Khamenei.




















