Rokoki sun fashe a birnin Isra'ila bayan barazanar Hamas

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

A'isha Babangida, Mukhtar Adamu Bawa, Rabiatu Kabir Runka and Haruna Kakangi

  1. 'Amurkawa 20 sun ɓata a Isra'ila'

    Joe Biden

    Asalin hoton, Getty Images

    Fadar White House ta yi bayanin cewa akwai Amurkawa 20 da suka bata bayan harin da Hamas ta kai wa Isra'ila, in ji mai ba Amurka shawara kan harkokin tsaro Jake Sullivan.

    Sai dai ya ce ba zai iya tabbatar da adadin mutanen da aka yi garkuwa da su ba.

    Gwamnatin Amurka ta dauki samun bayanai game da Amurkawa da suka bace da matuƙar muhimmanci, kuma tana tuntubar duk iyalan da abin ya shafa, in ji Sullivan.

    Tun da farko shugaban Amurka Joe Biden ya ce an san Amurkawa 14 ne aka kashe a hare-haren. Sullivan ya kuma nanata kudurin Amurka kan Isra'ila: "Wannan abu ne mai muhimmanci ga jama'ar Amurka saboda alakarsu da Isra'ila."

    • Amurka ta fara matsar da jiragen yaki kusa da Isra'ila bayan harin Hamas
    • Firaministan Isra'ila ya yi watsi da kiran shugaban Amurka
  2. Amurka ta dakatar da bai wa Nijar tallafi

    Niger

    Asalin hoton, Reuters

    Ƙasar Amurka za ta dakatar da mafi yawan tallafin da take baiwa Nijar bayan ta ayyana mamayar da sojoji suka yi a ƙasar a matsayin juyin mulki, tare da takaita ikonta na ba da agaji ga ƙasar da ke yammacin Afirka.

    A ciwata sanarwa da hukumomin Amurka suka fitar, sun ce za su ci gaba da bayar da wasu kayan agaji ga ƙasar.

    Amurka ta ce ta kare duk wata hanya na daidaita tsarin mulki a Nijar, kuma ba ta da wani zabi illa ta dakatar gudummawar sojojin da take baiwa Nijar.

    Za ta dakatar da duk wani taimakon da ba na jin kai ba, ciki har da horar da sojojin Nijar. Amma za ta ci gaba da amfani da jiragen sa ido kan kungiyoyin masu tsattsauran ra'ayi domin tabbatar da tsaron sojojin Amurka.

    Akwai kusan dakarun Amurka 1000 a Nijar wadanda za su cigaba da zama a ƙasar..

    Sanarwar da Amurka ta fitar na zuwa ne a daidai lokacin da sojojin Faransa 1500 ke shirin janyewa daga Nijar.

    Nijar ta kasance daya daga cikin manyan kawayen kasashen yamma a yankin Sahel da ake da kungiyoyin da ke da alaka da Al Qaeda da kuma IS. Amma bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a ranar 26 ga watan Yuli, gwamnatin mulkin soji ta bukaci sojojin Faransa da su fice, suna zarginsu da hada baki da kasashen yankin wajen maido da zababben shugaban ƙasar Mohamed Bazoum da ƙarfin tsiya

  3. Kotu ta daure wani manjo janar a kan laifin satar dukiyar Najeriya

    Nigerian Army

    Asalin hoton, NIgerian Army/Facebook

    Wata kotun sojoji ta musamman a Najeriya da ke zamanta a Abuja ta yanke hukunci ga wani babban hafsan sojin kasar Manjo Janar Umar Mohammed bayan ta same shi da laifin satar miliyoyin nairori daga kamfanin kula da kadarorin rundunar sojojin kasa.

    Tun da farko, kotun ta samu Janar Umar Mohammed da laifi kan 14 a cikin tuhuma 18 da aka yi masa. Babban sojan ya rike matsayin manajan daraktan kamfanin kula da kadarorin rundunar sojojin kasan Najeriya (Nigerian Army Properties Limited), inda aka same shi da laifin tafka sace-sace.

    Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa an yi wa Janar Umar Mohammed shari'a ne kan tuhuma 18 da ke da alaka da yin takardun jabu da fallasar da dukiyar al'umma da hada baki don aikata laifi da sauransu.

    Sai dai wanda ake zargin a baya ya musanta aikata dukkan laifukan da ake tuhumarsa da shi.

    Sai dai a zaman da aka ci gaba gudanarwa a ranar Talata inda aka yanke hukuncin, kwamitin mai mutum takwas karkashin jagorancin Maj.-Gen. James Myam, ya bayyana cewa an samu babban hafsan sojan da aka yankewa hukuncin da laifuka 14 cikin 18.

    Bayan haka, a hukuncin da ya yanke, kotun ta bayar da umarnin a daure babban jami’in da aka yanke wa hukuncin shekaru 5 a gidan yari bisa wasu laifuffukan da aka aikata, wasu kuma na da shekaru 7 akwai kuma masu dauke da hukunci shekara 2.

    Yayin da ake bayyana cewa hukuncin zai gudana ne a lokaci guda, kotun ta kuma umarce shi da ya mayar da wasu kudade a asusun hukumar NAPL.

    Kafin yanke masa hukunci, Mohammed ya kasance a wurin da ake tsare jami'a sojin Najeriya a barikin Mogadishu da ke Abuja inda ya shafe sama da shekaru 2 a tsare.

  4. Mazauna ƙauye sun cinye giwar da ta fito daga gandun daji

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Mazauna wani ƙauye da ke maƙwaftaka da gandun dajin Virunga a Jamhuriyar Demokuraɗiyyar Kongo sun kashe tare da cinye wata giwa da ta fito daga gandun dajin.

    Malaman daji sun ambato mazaunan ƙauyen da ake kira Katwiguru, waɗanda ke cike da murna na cewa "wannan tamkar nama ne daga sama gasasshe."

    Ƙungiyar masu aikin kare gandun dajin sun wallafa a shafinsu na tuwita cewar babu tabbas kan ko ƴan tawaye ne suka kashe giwar ko kuma mazauna ƙauyen.

    Kafar yaɗa labaru ta AFP ta ruwaito cewar a makonnin da suka gabata ne wasu matasa suka lalata shingen gandun dajin, lamarin da ya bai wa giwaye biyu damar ficewa.

    A yanzu ba a san wane hali ɗaya giwar take ciki ba.

    Virunga, wani shahararren gandun daji ne da ke tsakiyar yankin da ke fama da rikici kusa da iyaka da Uganda da kuma Rwanda.

    Shafin gandun dajin ya ce giwaye 589 ne suka shiga gandun dajin a shekarar 2020, lamarin da ya sanya yawan giwayen da ke cikin gandun dajin ya kai 700.

  5. Hotunan yadda dakarun Faransa suka fara ficewa daga Jamhuriyar Nijar

    Dakarun Faransa sun fara ficewa daga jamhuriyar Nijar a ranar Talata bayan jagororin mulkin sojin ƙasar sun umurce su da yin haka.
    Bayanan hoto, Dakarun Faransa sun fara ficewa daga jamhuriyar Nijar a ranar Talata bayan jagororin mulkin sojin ƙasar sun umurce su da yin haka.
    Fara ficewar dakarun na Faransa na zuwa ne daidai ranar da Amurka ta sanar da dakatar da tallafin kuɗi sama da dala miliyan 500 da take bai wa ƙasar domin taimaka mata wajen yaƙi da masu ikirarin jihadi a yankin Sahel.
    Bayanan hoto, Fara ficewar dakarun na Faramsa na zuwa ne daidai ranar da Amurka ta sanar da dakatar da tallafin kuɗi sama da dala miliyan 500 da take bai wa ƙasar domin taimaka mata wajen yaƙi da masu ikirarin jihadi a yankin Sahel.
    Mai magana da yawun shugaban ma'aikata na Faransa ya tabbatar wa kamfanin dillacin labaru na AFP cewar "Tawaga ta farko ta fice".
    Bayanan hoto, Mai magana da yawun shugaban ma'aikata na Faransa ya tabbatar wa kamfanin dillacin labaru na AFP cewar "Tawaga ta farko ta fice".
    Ya tabbatar da cewa sojojin Faransa 1,400 ne za su fice daga ƙasar, Farawa daga ranar Talata.
    Bayanan hoto, Ya tabbatar da cewa sojojin Faransa 1,400 ne za su fice daga ƙasar, Farawa daga ranar Talata.
  6. Tashin farashin Gas ɗin girki na ƙara damun magidanta a Najeriya

  7. 'Yan ta-da-kayar-baya sun kashe duk 'yan gidan daya a kauyen Isra'ila

    Masu aika rahotanni a yau Talata sun kai ziyara kauyen Kfar Aza - inda 'yan Hamas suka aikata kisan kare dangi a kusan da kan iyaka da Gaza.

    Kafin safiyar yau an ci gaba da gwabza fada a kibbutz. Abin da ya sa sai yanzu ne kawai sojoji suke kwashe gawawwakin wadanda aka yi kisan gilla.

    Sojoji sun fada wa editan BBC kan al'amuran kasashen duniya Jeremy Bowen cewa mayakan Hamas sun auka wa kauye, inda suka rika kona gidaje da kashe iyalai.

    Wani hafsan sojan Isra'ila ya ce wasu da suka mutu, fille musu kawuna aka yi.

    • Wace ce Hamas, mene ne ke faruwa a Isra'ila, da sauran tambayoyi
    • Ba za mu gushe ba har sai mun shafe Hamas daga doron kasa - Netanyahu
    Israel Soldiers

    Asalin hoton, Oren Rosenfeld

  8. Mamaye ta ƙasa a Gaza ba mafita mai sauƙi ba ce kan barazanar Hamas, Daga Frank Gardner Wakilin BBC a Fannin Tsaro

    Akwai raɗe-raɗi daga wasu sassa cewa, ta wata hanya ana iya kakkaɓe barazanar da Isra'ila ke fuskanta daga Hamas gaba ɗaya, idan aka yi amfani da cikakken mamayen sojoji ta ƙasa.

    Tarihi zai nuna cewa wannan mai yiwuwa ba mafita ce ta take-yanke ba, kamar yadda wasu suke fata.

    Lokacin da Isra'ila ta mamaye Gaza a 2014, an kashe Falasɗinawa fiye da 2,000, inda kowacce jana'iza ke ingiza ƙarin matasan da ke zama masu tsattsauran ra'ayi.

    Tun daga lokacin, Hamas ta ci gaba da harba rokoki zuwa tsallaken iyaka.

    An yi imani reshenta na 'yan gwagwarmaya da makamai, na da yawan mayaƙa kimanin 30,000, mafi yawansu 'yan gani-kashe-ni a kan ƙudurinsu na kare Falasɗinu.

    Sun san hanyoyin ƙarƙashin ƙasa da suka gina da ɗakunan ƙarƙashin ƙasa da gine-ginen ɓuya na ƙarƙashin ƙasa da kuma lungu da sakon Gaza fiye da sojojin mamaya.

    Irin wannan tsukukin yanki da ke maƙare da jama'a, ba wuri ne na tankokin yaƙi ba, waɗanda za su iya zama masu matuƙar rauni ga hare-haren kwanton ɓauna.

    Daga mahangar tsagwaron aikin soja, hari ta ƙasa zai haifar da nasarar wucin gadi, tare da kakkaɓe mafi yawan kwamandojin Hamas.

    Amma, da rashin wata yarjejeniyar zaman lafiya mai ɗorewa, akwai yiwuwar Hamas za ta iya sake tsirowa, ta gayyato wata sabuwar rundunar fusatattun matasa, mayaƙa sabbin jini masu tsattsauran ra'ayi.

  9. An ɗaure ƴar TikTok kan zagin shugaban ƙasa

    shugaba João Lourenco

    Asalin hoton, EPA

    Bayanan hoto, shugaba João Lourenco

    Wata mai faɗa a ji a shafukan sada zumunta a Angola za ta sha daurin shekaru biyu a gidan yari saboda "cin mutuncin" shugaba João Lourenco a kan TikTok.

    Kotu ta yankewa Ana da Silva Miguel, wanda aka fi sani da Neth Nahara, hukuncin ɗaurin watanni shida a watan Agusta.

    Sai dai wata kotun daukaka kara ta yanke cewa hukuncin ya kasance mai sassauci inda ta kara shi zuwa shekaru biyu.

    Ms Miguel ta zargi shugaban ƙasar a shafinta na TikTok da janyo "hargitsi da rashin tsari", in ji kafofin watsa labarai na cikin gida.

    Ta kuma jinginawa shugaban kasar laifin rashin makarantu da gidaje da kuma ayyukan yi a a kasar mai arzikin man fetur.

    Kotun daukaka karar da ke Luanda babban birnin ƙasar, ta ce Ms Miguel ta yi amfani da kalaman batanci ga shugaban ƙasar, kuma kasancewar ta na da ikon yin tasiri a kan ra'ayin jama'a ya karawa lamarin muni.

  10. Ƴan bindiga sun sace ɗaliban Jami’ar Nasarawa

    Nasarawa State University

    Asalin hoton, iStock

    Ƴan bindiga sun yi awon-gaba da ɗalibai huɗu na jami’ar jihar Nasarawa da ke garin Keffi.

    Bayanai sun nuna cewa an sace ɗaliban ne ranar Talata a lokacin da wasu ƴan bindiga suka kai samame a gidajen kwanansu da ke Anguwar Kare, a karamar hukumar Keffi.

    Jami’in hulda da jama’a na rundunar ƴan sanda a jihar, DSP Ramhan Nansel, ya tabbatar da lamarin a wata tattaunawa ta wayar tarho.

    Ya ce da sanyin safiyar Talata ne rundunar ƴan sanda a jihar ta samu kiran gaggawa cewa wasu ƴan bindiga sun kai hari a wani gida a Anguwar Kare.

    “Rundunar tana sane da sace mutanen da aka yi da misalin karfe 12:55 na dare yayin da aka samu rahoton cewa wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba suka mamaye wani gida da ke Anguwar Kare, Keffi,” inji Nansel.

    Kokarin da aka yi na bin sawun wadanda suka aikata laifin ya ci tura amma an fara farauta domin kuɓutar da ɗaliban, in ji kakakin ‘yan sandan.

    • Yadda aka karbo mutum 75 daga hannun 'yan bindiga a Zamfara
    • Muna fama da karuwar hare-haren 'yan bindiga a yankinmu'
  11. Isra'ila ta ce an kashe manyan jami'an Hamas biyu a hare-hare ta sama

    Manyan jami'an kungiyar Hamas biyu sun mutu a hare-hare ta sama a Gaza, cewar rundunar sojin Isra'ila.

    Zakaria Abu Muammar da Jawad Abu Shamal, jami'ai a ofishin harkokin siyasa na Hamas, sun mutu bayan wani samame a Khan Yunis da sanyin safiyar nan, in ji rundunar tsaron Isra'ila.

    Wani mai magana da yawun rundunar ya ce Jawad Shamal ne ministan harkokin tattalin arziki na kungiyar Hamas, kuma yana da hannu cikin "harkokin samar da kudi don gudanar da ayyukan ta'addanci a ciki da wajen Zirin Gaza" da kuma jagorantar ayyukan da ake kai wa kan 'yan kasar Isra'ila.

    Zakaria Muammar kuwa shi ne shugaban ofishin hulda da kasashen wajen Hamas, kuma yana da hannu wajen tsara "ayyukan ta'addanci da dama", kamar yadda rundunar sojin Isra'ila ta yi zargi.

    Hamas ba ta tabbatar da mutuwar mutanen biyu ba, kuma a karan kanta ba ta iya tabbatar da ikirarin na Isra'ila ba.

    • Sahihan bidiyon harin da Hamas ta ƙaddamar kan Isra'ila
    • Mummunan harin ba-zata da Hamas ta kaddamar a kan Isra'ila
  12. BIDIYO: Rokokin da aka harba daga Gaza bayan gargadin Hamas

    Wannan hoton bidiyo daga kamfanin dillancin labarai na Reuters na nuna rokokin da ake harbawa daga Zirin Gaza jim kadan bayan karfe 5 na yamma agogon yankin daidai da karfe 3 na rana agogon Najeriya.

    Wakiliyar BBC Alice Cuddy da ke birnin Ashkelon ita ta ji tashin rokokin a daidai wannan lokaci - bayan kungiyar Hamas ta gargadi mutane su fice daga birnin.

    Bayanan bidiyo, Bidiyo: Makaman roka da aka harba daga Gaza zuwa kudancin Isra'ila
  13. Gwamnatin Katsina ta kaddamar da matasa 'yan sintiri don yaki da 'yan fashin daji

    Ga hotunan bikin kaddamar da daruruwan matasa 'yan sintiri da gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya yi ranar Talata a birnin Katsina

    Katsina Vigilante

    Asalin hoton, Alfijir Radio

    Bayanan hoto, Gwamnatin Katsina ta kaddamar da rundunar 'yan sintirin ce mai matasa 1,500, a matsayin wani mataki na karfafa gwiwar al'ummar garuruwa su kare kansu daga hare-haren ta'addanci.
    Katsina Vigilante

    Asalin hoton, Alfijir Radio

    Bayanan hoto, Katsina na cikin jihohin Arewa maso Yammacin Najeriya da ke fama da matsalar rikicin 'yan ta-da-kayar-baya, da ke kai hari a kan kauyuka da matafiya, inda suke kashewa da jikkatawa da kuma sace wasu don neman kudin fansa.
    Katsina Vigilante

    Asalin hoton, Alfijir Radio

    Bayanan hoto, Rundunar wadda aka yi wa lakabin jami'an sintiri na garuruwa za su yi aiki kafada-da-kafada da jami'an tsaron Najeriya a jihar Katsina wajen tunkarar 'yan fashin daji da ke addabar garuruwa.
    Katsina Vigilante

    Asalin hoton, Alfijir Radio

    Bayanan hoto, Matasa 'yan sintirin sun samu horo tsawon lokaci kafin a kaddamar da su, gwamnati kuma daga bisani za ta tura su zuwa sassan jihar don karfafa tsaro.
    Katsina Vigilante

    Asalin hoton, Alfijir Radio

    Bayanan hoto, Gwamna Dikko Umar Radda ya samar da motoci da baburan sintiri ga rundunar tsaron ta cikin gida don inganta ayyukansu a fadin jihar.
  14. Fashewar rokoki a birnin da ke kusa da Zirin Gaza

    Wakiliyarmu Alice Cuddy tana ci gaba da kawo rahotanni game da rokokin da suke tashi a Ashkelon.

    Matakin na zuwa ne bayan kungiyar Hamas mai gwagwarmaya da makamai ta kai hare-hare kan birnin.

    Ga wata taswira da ke nuna inda birnin yake a kudancin Isra'ila - a kusa da Zirin Gaza, wanda tunga ce ta al'ummar Falasdinawa.

    ..

    Asalin hoton, ..

  15. Martanin ƙasashen Afirka kan rikicin Isra'ila da Falasɗinawa

    ...
  16. Labarai da dumi-dumi, Makaman roka sun dira a birnin Ashkelon bayan wa'adin Hamas

    An ji karar fashewar rokoki da dama, daidai lokacin da wa'adin da kungiyar Hamas ta bayar na karfe 5 na yamma agogon yankin, cewa mazauna birnin Ashkelon su fice, ya cika.

    Wakiliyar BBC Alice Cuddy daga birnin Ashkelon ta ce suna tare da wasu mazauna birnin a gidan da suke fakewa.

    Dukkansu, a cewarta suna duba wayoyin salula tare da jira cikin zakuwa don ganin abin da zai faru a gaba.

    Ta ce sun ji karin fashewar abubuwa a cikin 'yan mintunan da suka wuce.

  17. Najeriya ta kwaso Kiristocin da suka je kasar Isra'ila aikin ibada

    Christian pilgrims

    Asalin hoton, Babajide Sanwo-Olu/X

    Gwamnan jihar Lagos ya bayyana farin ciki da komawar Kiristoci maniyyata 310 zuwa gida bayan sun je birnin Jerusalem na kasar Isra'ila don yin aikin ibada.

    Babajide Sanwo-Olu ya ce sun yi nasarar kwaso dukkan Kiristoci maniyyata aikin ibadar zuwa gida Lagos.

    Gwamnan ya yaba wa ma'aikatar harkokin cikin gida ta Najeriya saboda abin da ya kira aiki mai kyau da suka yi wajen mayar da masu zuwa aikin ibadar birnin Jerusalem, gida Lagos.

    Duk shekara, Kiristoci daga Najeriya kan je ziyarar ibada zuwa birnin Jerusalem na Isra'ila.

    Kungiyar Hamas ta kaddamar da hare-haren da ba a taba ganin irinsu ranar Asabar a kan Isra'ila, inda ta kashe mutane tare da yin garkuwa da wasu ciki har da sojoji da mata da kananan yara.

    Nigerian Christian pilgrims

    Asalin hoton, Babajide Sanwo-Olu/X

  18. Ga yadda masu zaɓe ke kada kuri'a a Laberiya

    ...

    Ana ci gaba da zaɓen shugaban ƙasa da na ƴan majalisar dokoki a Laberiya.

    Ƴan takara 19 ne dai ke fatan maye gurbin shugaban ƙasar Gorge Weah wanda shima ke neman wa'adi na biyu.

    Ga hotunan yadda masu zaɓe ke kada kuri'a a ƙasar.

    ...
    Bayanan hoto, Gorge Weah ya fito kada kuri'a
    ...
    Bayanan hoto, Mutanen Laberiya a kan layi suna jiran kada kuri'arsu
    ...
    Bayanan hoto, Wata mata ta gama kada kuri'arta
    ...
    Bayanan hoto, Wasu suna raka wani tsoho zuwa wajen kada kuri'a
    ...
  19. Hamas ta gargadi mazauna Ashkelon su fice daga birnin

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hamas ta yi barazanar kai hari musamman a birnin Ashkelon na Isra'ila, a matsayin martani ga hare-haren da Isra'ila ke kai wa Zirin Gaza.

    A wani sako da ta wallafa a kafar sada zumunta ta Telegram, Hamas ta ce mazauna birnin Ashkelon da ke arewacin Zirin Gaza su fice daga yankin.

    Makaman roka fiye da 4,500 ne aka harba daga Gaza zuwa Isra’ila tun ranar Asabar, in ji rundunar sojin Isra’ila.

  20. Mutane na kwana a waje bayan zaftarewar kasa a Kamaru

    ...

    Wani mutum wanda yaronsa ke daya daga cikin akalla mutum 30 da suka mutu a zabtarewar ƙasar da ta faru a Yaounde, babban birnin Kamaru, ya ce ya kwana cikin sanyi a waje saboda shi da iyalinsa ba su samu mafaka a wani wurin ba.

    Ymele Guy, mazaunin unguwar Mbankolo ne ta masu karamin karfi, inda gidaje da gine-gine da dama suka ruguje bayan ruwan sama kamar da bakin kwarya a ranar Lahadi ya haddasa zaftarewar ƙasa.

    Jami’an da suka kai ziyara sun ba shi katifa tare da matarsa ​​da ‘ya’yansa uku da suka tsira, inda suka sanar da su sauran gidajen da suka rage a yankin duk za a rushe su.

    Ministar gidaje Célestine Ketcha Courtès ta fada a yayin ziyarar da ta kai ranar Litinin cewa, za a samar da matsuguni na wucin gadi a zauruka da sauran wuraren taruwar jama'a ga wadanda ba su da makwanci.

    "Muna da matsaloli da yawa, muna kwana a waje saboda hukumomi sun ce dole ne su ruguza komai. Ba ni da wanda zan iya kwana a wurinsa," in ji Guy.

    Yankin gida ne ga mutane da yawa da ke ƙaura zuwa babban birnin ƙasar bayan sun baro yankunan karkara don neman aiki.

    • Me ke jawo ambaliyar ruwa kuma me za ku yi don kare kanku?
    • Iyalai da dama na cikin tsaka mai wuya sakamakon ambaliyar ruwa a birnin Damaturu