Buga gyam ya kai ni ƙasashen waje - matashi ɗan Najeriya

Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyon
Buga gyam ya kai ni ƙasashen waje - matashi ɗan Najeriya

Farouk Manzo, matashi ne da ya ƙware wajen buga wasannin gyam (game) a kan kwamfiyutarsa, inda har ya mayar da baiwar da yake da ita sana'a.

Matashin mai shekara 21 ya ce buga wasannin gyam ya kai shi ƙasashen duniya kamar Faransa da Masar da Ivory Coast.

Ya ce wasan gyam bai hana shi neman ilmi ba, inda zuwa yanzu ya karanta fannin tattalin arziƙi.

Ya ce a wannan shekara ma, yana shirin zuwa ƙasar Saudiyya don buga gyam