'Wasu na kusa da Tinubu ne ke hana a cire wa Nijar takunkumai'

Bayanan sautiLatsa hoton sama ku saurari shirin:
'Wasu na kusa da Tinubu ne ke hana a cire wa Nijar takunkumai'

Shirin Gane Mini Hanya na wannan makon ya yi tattaunawa ta musamman da Firaministan Nijar Ali Lamine Zeine, wanda sojoji suka naɗa.

Firaministan ya taɓo batutua da dama, ciki har da batun cire musu takunkuman da Ecowas ta ƙaƙaba wa ƙasar bayan juyin mulkin da sojojin suka yi a watan Yuni.

Ya yi zargin cewa akwai "wasu ƙwararru" na kusa da Shugaban Najeriya Bola Tinubu "da ke mayar da hannun agogo baya" game da takunkuman a matsayinta na jagorar Ecowas.